Wasanni

Kocin Kano Pillars, Usman Abdallah ya ajiye aikinsa

Kocin Kano Pillars, Usman Abdallah ya ajiye aikinsa

Babban kocin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars, Usman Abdallah, ya ajiye aikinsa na horas da tawagar a ranar Laraba, kamar yadda sashen yaɗa labarai na ƙungiyar ya tabbatar da hakan. Sanarwar da aka fitar da yammacin ranar Laraba ta bayyana cewa Abdallah ya yanke shawarar barin muƙaminsa ne da kansa, sai dai bai bayyana dalilan da suka sanya shi ɗaukar wannan mataki ba. A halin da ake ciki, magoya bayan Pillars na ci gaba da bayyana ra’ayoyinsu a kafafen sada zumunta dangane da ficewar Abdallah, inda da dama ke bayyana fatan ganin sabon babi mai armashi a tarihin ƙungiyar.
Read More
Senegal ta zama ƙasar Afrika ta farko da ta doke Ingila a wasan ƙwallon ƙafa

Senegal ta zama ƙasar Afrika ta farko da ta doke Ingila a wasan ƙwallon ƙafa

Daga USMAN KAROFI A wani fafatawa na sada zumunta da aka buga a daren Talata a filin wasa na City Ground, ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Senegal ta lallasa Ingila da ci 3-1, abin da ya sa ta kafa tarihi a matsayin ƙungiya ta farko daga nahiyar Afirka da ta doke Ingila. Harry Kane ne ya fara zura ƙwallo a ragar Senegal bayan ɗan wasan gaban Ingila, Anthony Gordon, ya gwada bugun da mai tsaron ragar ya mayar, amma Ismaila Sarr ya farke ƙwallon kafin ƙarshen rabin lokaci. A zagaye na biyu, Habib Diarra ya ƙara ci gaba da jefa ƙwallon…
Read More
Fulham ta sanar da korar William da Carlos Vinicius

Fulham ta sanar da korar William da Carlos Vinicius

Fulham ta sanar cewa, Willian da Carlos Vinicius za su bar ƙungiyar bayan da yarjejeniyarsu za ta ƙare a ƙarshen watan Yuni. Willian, wanda ya sake komawa Fulham a farkon shekarar nan ya buga wasa 79 tun bayan da ya fara buga mata tamaula a 2022 a karon farko.Shi kuwa Vinicius zai yi ban kwana da Fulham, bayan da suke su uku a gurbin da yake bugawa, idan aka haɗa da Raul Jimenez da Rodrigo Muniz. Fulham ta yi wa kyaftin ɗinta Tom Cairney tayin karin kwantiragi, wanda ake alaƙanta shi da zai koma Wrexham, wadda za ta buga gasa…
Read More
Inzaghi ya karɓi aikin horar da Al-Hilal kwana guda bayan ficewarsa daga Inter

Inzaghi ya karɓi aikin horar da Al-Hilal kwana guda bayan ficewarsa daga Inter

An naɗa Simone Inzaghi a matsayin kocin ƙungiyar ƙwallon ƙafar Saudiyya ta Al-Hilal, kwana guda bayan barin Inter Milan. Kocin na Italiya ya rattaba hannu kan kwantiragin shekaru biyu bayan ya bar Inter ranar Talata. Kulob ɗin ta Serie A ta sha kaye da ci 5-0 a wasan ƙarshe na gasar kofin zakarun Turai da suka doka ranar Asabar da Paris St-Germain, abin da ke nuna irin rashin lashe kofuna da ƙungiyar da fama da shi tun 2019-20. Inzaghi ya karɓi ragamar horar da Inter a shekarar 2021, inda ya jagoranci Nerazzurri zuwa gasar lig ta 2023-24 kuma ya lashe…
Read More
Arsenal za ta yi ban-kwana da ’yan wasa 20

Arsenal za ta yi ban-kwana da ’yan wasa 20

’Yan wasa Jorginho da Kieran Tierney za su bar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal, bayan da kwantiraginsu ya ƙare a ranar 30 ga watan Yuni, 2025, waɗanda ta sanyaa jaddawalin waɗanda ba ta buƙatar su. Jorginho, wanda ɗan wasan tawagar Italiya ne da ke dab da rattaba hannu a Flamengo ta Brazil, ya koma Emirates ne daga Chelsea a Janairun 2023, inda ya yi mata wasa 79. Shi kuwa Tierney, ɗan tawagar Scotland, ya koma Arsenal daga Celtic ne kaka shida da suka gabata, inda ya buga wasa 170, kana daga baya ya je aro a Real Sociedad a kakar…
Read More
’Yan wasa 10 mafi daraja a duniyar ƙwallon ƙafa

’Yan wasa 10 mafi daraja a duniyar ƙwallon ƙafa

Matashin ɗan wasan Barcelona, Lamine Yamal ka iya kai darajar kusan fam miliyan 340, idan za a sayar da shi, a cewar wata ƙungiya a ƙasar Switzerland mai nazari kan darajar ’yan wasa. A wata ƙididdiga ta daban, cibiyar sanya idanu kan ’yan wasa ta CIES, ta ƙiyasta cewa ɗan wasan mai shekara 17 zai kai darajar euro miliyan 400 - kusan ninkin abin da aka sayar da Barcelona ta sayar da Neymar - yuro miliyan 222 - ga PSG a 2017, mafi tsada a lokacin. Matashin ɗan Sifaniya ya kasance na biyar cikin jerin matasan ’yan ƙwallo da suka…
Read More
Osimhen ya bayyana kulob ɗin da ba zai taɓa zuwa ba

Osimhen ya bayyana kulob ɗin da ba zai taɓa zuwa ba

Ɗan wasan gaba na Super Eagles, Victor Osimhen, ya bayyana cewa zai fi so ya cigaba da zama a Galatasaray fiye da komawa Juventus. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta danganta shi da komawar zuwa tsohuwar zakarun Serie A, duk da yana kan aro daga Napoli zuwa Galatasaray. Wani masani daga kulob din Galatasaray, Yakup Çınar, ya ce Osimhen ya nuna rashin sha’awar komawa Italiya, inda ya ce: “Juventus na son Osimhen, amma ya ce zai fi son zama a Galatasaray.” Ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da ya yi a tashar YouTube ta Yeni…
Read More
Al Nassr ta buƙaci Ronaldo ya ci gaba da zama a ƙungiyar

Al Nassr ta buƙaci Ronaldo ya ci gaba da zama a ƙungiyar

Daraktan wasannin Al Nassr, Fernando Hierro ya sanar a ranar Alhamis cewa suna yin iya ƙoƙarinsu domin Cristiano Ronaldo ya ci gaba da buga musu wasa Ya faɗi hakan ne bayan wasu rahotannin da aka ce ɗan Portugal ɗin zai buga FIFA Club World Cup da za a fara daga 14 ga watan Yuni a Amurka. A makon jiya Wydad Casablanca ta musanta batun da ake cewar ta ɗauki Ronaldo, domin ya ja ragamar ƙungiyar a Fifa Club World Cup a bana. Ranar Litinin bayan da aka kammala gasar ƙwallon ƙafa ta Saudiyya, Ronaldo ya sanar a ɗ cewa, ''An…
Read More
Conference League: Chelsea ta murƙushe Real Betis a wasan ƙarshe

Conference League: Chelsea ta murƙushe Real Betis a wasan ƙarshe

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea ta lashe kofin UEFA Conference League bayan doke Real Betis da ci 4-1 a wasan ƙarshe da aka buga ranar Laraba. Wannan shine karo na farko da ƙungiyar ta samu kofi a ƙarƙashin sabon kocinta Enzo Maresca. Real Betis ce ta fara jefa ƙwallo a ragar Chelsea a minti na 9 ta hannun dan wasan Morocco, Abde Ezzalzouli, bayan wani kyakkyawar bugun baya daga Isco. Sai dai bayan hutun rabin lokaci, Chelsea ta dawo da ƙarfi inda Enzo Fernandez, Nicolas Jackson, Jadon Sancho, da Moises Caicedo suka zura ƙwallaye huɗu. Wannan nasara ta kawo ƙarshen…
Read More
Najeriya ta casa Ghana a wasan kofin Unity

Najeriya ta casa Ghana a wasan kofin Unity

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Najeriya, Super Eagles, ta doke Ghana da ci 2-1 a wasan kusa da na ƙarshe na Unity Cup da aka buga a Gtech Community Stadium, London. Cyriel Dessers ne ya fara jefa ƙwallo a minti na 14 da taimakon S. Ismail. Bayan mintuna biyar, ɗan wasan Ghana Razak Simpson ya ci ƙwallon kansa wanda ya ƙara wa Najeriya gagarumin rinjaye. Ghana ta samu nasarar jefa ƙwallo guda a minti na 70 ta hannun ɗan wasanta Thomas-Asante, wanda hakan ya sa wasan ya ƙare da ci 2-1. Wannan nasara ta bai wa Super Eagles damar samun gurbi…
Read More