17
May
Daga USMAN KAROFI Ƙungiyar Crystal Palace ta kafa tarihi bayan da ta doke Manchester City da ci 1-0 a wasan ƙarshe na FA Cup da aka buga a filin wasa na Wembley. Wannan ne karo na farko da ƙungiyar daga kudancin London ta lashe babban kofi cikin shekaru 120 da kafuwarta. Ɗan wasan gaba Eberechi Eze ne ya zura ƙwallon nasara a minti na 16 da fara wasa. Manchester City ta samu damar farkewa a minti na 33 bayan da aka basu bugun daga kai sai mai tsaron gida, amma Dean Henderson ya hana Omar Marmoush cin ƙwallon. A minti…
