Wasanni

Crystal Palace ta doke Manchester City a wasan ƙarshe na gasar FA

Crystal Palace ta doke Manchester City a wasan ƙarshe na gasar FA

Daga USMAN KAROFI Ƙungiyar Crystal Palace ta kafa tarihi bayan da ta doke Manchester City da ci 1-0 a wasan ƙarshe na FA Cup da aka buga a filin wasa na Wembley. Wannan ne karo na farko da ƙungiyar daga kudancin London ta lashe babban kofi cikin shekaru 120 da kafuwarta. Ɗan wasan gaba Eberechi Eze ne ya zura ƙwallon nasara a minti na 16 da fara wasa. Manchester City ta samu damar farkewa a minti na 33 bayan da aka basu bugun daga kai sai mai tsaron gida, amma Dean Henderson ya hana Omar Marmoush cin ƙwallon. A minti…
Read More
 Bologna ta lashe kofin Italiya bayan doke AC Milan

 Bologna ta lashe kofin Italiya bayan doke AC Milan

Bologna ta lashe gasar kofin Italiya a ranar Laraba bayan da ta doke AC Milan da ci 1-0 a birnin Rome kuma ta kawo ƙarshen shekaru 51 da ta shafe tana jiran lashe babban kofi. Dan wasa Ndoye ne ya zura ƙwallon a minti na 53 da fara wasan wanda ya baiwa Bologna nasara mai cike da tarihi, wanda kuma shi ne karramawar da suka samu tun bayan lashe kofin ƙarshe a shekarar 1974. Bologna ba ta ma shiga babbar gasa ta ƙarshe ba tun bayan da ta lashe kofin Italiya na ƙarshe - karo na biyu a gasar kofin…
Read More
Gwamnatin Katsina ta bada miliyan N99 don gyara filin wasan Funtuwa 

Gwamnatin Katsina ta bada miliyan N99 don gyara filin wasan Funtuwa 

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnatin Jihar Katsina ta amince da bada Naira miliyan 99 don gyara filin wasan ƙwallon ƙafa na garin Funtuwa. Kwamishinan wasanni Aliyu Zakari Shargalle ya sanar da haka a garin Funtua lokacin da yake miƙa takardar kwantaragin ga ɗan kwangilan. Ya sanar da cewa Gwamna Dikko Raɗɗa ne ya bada kwangilar aikin ganin yadda filin wasan ke da muhimmanci wajen haɓaka wasanni a jihar. Aliyu Zakari ya bayyana cewa ayyukan da za a yi a filin wasan ya haɗa da gina magudanan ruwa, katangar filin wasan da waya da sanya ciyawa irin wanda ake sawa…
Read More
Fafatawar El-Clasico ce za ta yanke hukunci kan La Liga – Ancelotti

Fafatawar El-Clasico ce za ta yanke hukunci kan La Liga – Ancelotti

Kocin Real Madrid, Carlo Ancelotti ya bayyana muhimmancin fafatawar wasan hamayya ta El-Clasico ga Real Madrid a fatan da take na lashe kofin Laliga a bana. A ranar Lahadi ne Real Madrid ta doke Celta Vigo 3-2, inda yanzu maki huɗu ne tsakaninta da Barcelona da ke jan ragamar teburin LaLiga. Kocin ya ce wasan Clasico ne zai iya yanke hukunci kan hamayyar kofin LaLiga. Idan Madrid ta samu sa'ar doke Barcelona zai kasance maki ɗaya ne tsakaninsu, yayin da ya rage wasa huɗu a kammala kakar bana. "Tabbas, ba zan ce wasan ranar Lahadi zai zama raba gardama ba,…
Read More
Liverpool ta lashe gasar Firimiya ta ƙasar Ingila karo na 20

Liverpool ta lashe gasar Firimiya ta ƙasar Ingila karo na 20

Ƙungiyar Liverpool ta sake lashe gasar Firimiya karo na biyu cikin shekaru biyar, inda yanzu haka ta daidaita da Manchester United wajen lashe kofin gasar Ingila sau 20 – mafi yawa a tarihi. A ranar Lahadi, Liverpool ta doke Tottenham da ci 5-1, wanda ya tabbatar musu da sabon kambun. Sabon koci Arne Slot ya jagoranci nasarar Liverpool a kakarsa ta farko a Ingila, inda ya zama kocin biyar da ya lashe gasar Firimiya a zangonsa na farko. Kafin shi, Jose Mourinho (Chelsea, 2005), Carlo Ancelotti (Chelsea, 2010), Manuel Pellegrini (Manchester City, 2013) da Antonio Conte (Chelsea, 2017) ne suka…
Read More
Gwamnatin Katsina ta dakatar da hukumar ƙwallon ƙafa ta Katsina United

Gwamnatin Katsina ta dakatar da hukumar ƙwallon ƙafa ta Katsina United

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Wannan mataki da gwamnatin Katsina ta ɗauka ya biyo bayan shan kaye da kungiyar ta sha a hannun ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta lkorodu City da ci shida ba ko ɗaya a gasar firimiya ta ƙasa. Mambobi kungiyar da aka dakatar sun haɗa da Ghaddafi Muahammar Ruduwan da Abbas Tukur sai Abdullahi Umar leda. Sauran sun haɗa da Yasir Yahaya da Abubakar Adidas tare da umurtan su da su miƙa kayayyakin ƙungiyar da ke hannu su zuwa ga babban sakataren a ma'aikatar matasa da wasanni Alhaji Rabiu Muhammad Rabiu. Kwamishinan harkokin matasa da wasanni Aliyu lawal…
Read More
Matic ya kira Onana ‘ɗaya daga cikin masu tsaron raga mafi muni a tarihin Man United’

Matic ya kira Onana ‘ɗaya daga cikin masu tsaron raga mafi muni a tarihin Man United’

ɗan wasan tsakiya na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Lyon, Nemanja Matic ya kira Andre Onana a matsayin "ɗaya daga cikin masu tsaron gida mafi muni a tarihin Manchester United". A ci gaba da fafatawar da koci Ruben Amorim ke fafutukar yi a Man United, Onana ya yi magana da manema labarai da tabbaci game da yuwuwar ƙungiyarsa ta doke Lyon a wasan daf da na kusa da na ƙarshe na gasar Europa, inda aka buga wasan farko a Faransa ranar Alhamis da daddare. "Dukkanmu mun san muhimmancin wannan wasan, za mu je can da tunanin yin nasara," kamar yadda ya…
Read More
Arsenal ta lallasa Real Madrid a Gasar Zakarun Turai

Arsenal ta lallasa Real Madrid a Gasar Zakarun Turai

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta doke Real Madrid da ci 3-0 a wasan daf da na kusa da ƙarshe na Gasar Zakarun Turai da aka buga a daren Talata a filin wasa na Emirates. Bayan kashi na farko ya ƙare babu ci, Arsenal ta fito ƙarara a zagaye na biyu inda Declan Rice ya zura ƙwallo biyu a raga, sannan Mikel Merino ya ƙara ta uku da ke bai wa ‘yan Ingila babbar dama kafin karawar dawowa a mako mai zuwa. A wani wasa da aka buga a daren, Inter Milan ta lallasa Bayern Munich da ci 2-1. Lautaro…
Read More
Tinubu ya rattaba hannu kan dokar hana amfani da ƙwayoyin ƙara kuzari a wasanni

Tinubu ya rattaba hannu kan dokar hana amfani da ƙwayoyin ƙara kuzari a wasanni

Shugaban Hukumar Wasanni ta ƙasa (NSC) Mallam Shehu Dikko, a madadin ɗaukacin masu ruwa da tsaki a harkokin wasanni, ya miƙa godiyarsa ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa rattaba hannu a kan ƙudirin dokar hana amfani da kwayoyi masu ƙara kuzari. A cewar shugaban NSC da ya rattaba hannu kan ƙudirin dokar, wanda aka shafe kusan shekaru 20 ana gudanar da shi, a cikin doka yana ƙarfafa niyyar shugaba Tinubu don tabbatar da cewa al’ummar ƙasar sun yi daidai da ƙa’idojin yaai da ƙwayoyin ƙara kuzari a duniya da kuma ci gaban wasanni gaba ɗaya. A cewarsa, “Ina godiya…
Read More
Barcelona ba ta da ikon yi wa Olmo rajista, inji La Liga

Barcelona ba ta da ikon yi wa Olmo rajista, inji La Liga

La Liga ta ce, Barcelona ba ta da ikon yin rijistar 'yan wasa Dani Olmo da Pau Victor, gabanin shawarar da hukumar wasanni ta Sifaniya (CSD) ta yanke kan cancantar 'yan wasan biyu na doka wasa. A watan Janairu Barcelona ta sanar da cewa an cimma yarjejeniyar sayar da manyan akwatina a filin wasa na Camp Nou, wanda a halin yanzu ake sake ginawa, wanda kuɗinsa ya kai Yuro miliyan 100 (dala miliyan 108), wanda ya ba su damar baje kolin kuɗi na sayen sabbin 'yan wasa. La Liga ta ce Barcelona ta yi amfani da wani mai binciken kuɗi…
Read More