Hukumar Zaɓe ta Katsina ta sanar da ranar gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi

Spread the love

Daga UMAR GARBA a Katsina

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Katsina (KATSIEC) ta saka ranar 15 ga watan Fabrairu, 2025 a matsayin ranar gudanar da zaɓukan shugabannin ƙananan hukumomi da kansilolo a jihar.

Shugaban hukumar, Lawal Alhassan Faskari ne ya bayyana haka a wurin taron masu ruwa da tsaki kan zaɓen wanda ya gudana a hedikwatar hukumar dake G.R.A.

A cewar shi, jam’iyyu masu rajista ne kawai za a bari su tsayar da ‘yan takara a kujeru daban-daban.

Alhaji Lawal Alhassan ya ce sashe na 28 na dokar zaɓen Nijeriya da aka yi wa gyaran fuska 2022 ne ya tanadi cewa a sanar da zaɓen kwanaki 365 gabanin gudanar da shi.

Ya ƙara da cewa nan gaba za su raba takardun da ke ƙunshe da ƙa’idoji da dokoki da kuma tsare-tsaren zaɓen.

“Dukkan masu sha’awar tsayawa takara da suka cancanta daga jam’iyyun siyasa masu rijista za su iya tsayar da ‘yan takara a muƙamin chayamomi da kansiloli bayan sun cika dukkan sharuɗɗan takarar.

” Yan takarar da jam’iyya ta ɗauki nauyinsu ne kawai za a bari su shiga zaɓen.” Inji shi.

Ya yi kira ga jami’an tsaron jihar akan su samar da tsaro lokacin gudanar da zaɓen musamman ƙananan hukumomin dake fuskantar matsalar tsaro.

By Editor