Ku haɗa kai wajen yaƙi da ‘yan ta’adda da ta’addanci, Shugaban APC na ƙasa ga ‘yan Nijeriya

Daga BASHIR ISAH

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Sanata Abdullahi Adamu ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da a haɗe kai wuri guda sannan a yaƙi ‘yan ta’adda da ta’addancinsu a faɗin ƙasa.

Sanata Adamu ya yi wannan kira ne biyo bayan mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai wa jirgin ƙasa a hanyar Abuja zuwa Kaduna a ranar Litinin da ta gabata.

Cikin sanarwar da ya fitar a jiya Laraba, Shugaban APCn ya ce lokaci ya yi da ya kamata ‘yan ƙasa su haɗa kai wajen yaƙar maƙiyan ƙasa.

Daga nan, ya nuna alhininsa dangane da rashe-rashen da kuma raunukan da aka samu yayin harin tare da miƙa ta’aziyyarsa ga ahalin marigayan.

A cewar Sanata Adamu, “Na yi Alla-wadai da wannan harin. Lamarin ya munana, kuma harin ya nuna yadda maƙiya za su yi dukkan mai yiwuwa wajen lalata ƙoƙarin da gwamanati ke yi wajen tabbatar da Nijeriya a matsayin ƙasa mai cikakken tsaro.

“Ina kira ga ‘yan Nijeriya su kalli wannan hari a matsayin aikin ‘yan ta’adda, maɓarnata waɗanda ba su ƙaunar zaman lafiyar ƙasar nan.

“Dole ne mu dunƙule mu yaƙi waɗanda ke lalata cigaban ƙasa da kuma dimukraɗiyyarmu.”