Daga BASHIR ISAH
Majalisar Dattawa ta ce ta kimtsa domin gayyato Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya zo ya yi bayani game da tabarbarewar tsaro a Birnin Tarayya.
Sanata mai wakiltar Birnin Tarayya a Majalisar, Ireti Kingibe ce ta bayyana haka yayin wata tattaunawa da tashar Channels TV ta yi da ita a ranar Lahadi.
Ta ce idan majalisar ta dawo bakin aiki, za a gayyato Wike a matsayinsa na Ministan Abuja don ya zo ya yi bayanin matakan da yake dauka domin dakile matsalar taro a birnin na tarayya.
A cewar Sanatar, “Ina da yakinin za a gayyace shi. Amma amsawa ko kin amsar gayyatar wani abu ne daban. Sai dai a matsayinsa na babban shugaban tsaro na FCT, dole ya zamana yana da tsari.
“Wajibi ne ya yi mana bayani mu ‘yan kwamiti, musamman ni, tsare-tsaren da ya shirya amfani da su don kare rayukan al’umar yankin Abuja.
“Dole ne a samu tsare-tsare a tsakaninsa da Kwamishinan ‘Yansada da shugaban DSS” don dakile matsalar tsaro a Abuja, in ji Sanata Iteti.
A baya-bayan nan, rahotanni daga yankin Abuja sun ce ana fama da matsalar tsaro, musamman garkuwa da mutane a birnin na tarayya.