Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanar da ma’aikatun da ministocinsa za su riƙe.
A ranar Laraba Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana jerin sunayen sabbin ministocin da kuma ma’aikatar da kowannensu zai jagoranta:
Ga jerin sunayen ministcoin da ma’aikatunsu:
Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin na Zamani – Bosun Tijani
Ƙaramin Ministan Muhalli – Ishak Salaco
Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki – Wale Edun
Ministar Harkokin Teku da Tattalin Arziki – Bunmi Tunji
Ministan Lantarki – Adedayo Adelabu
Ƙaramin Ministan Lafiya da Walwalar Al’umma – Tunji Alausa
Ministan Ma’adinai – Dele Alake
Ministan Yawon Buɗe-Ido – Lola Ade-John
Ministan Sufuri – Adegboyega Oyetola
Ministan Kasuwanci da Zuba Jari – Doris Anite
Ministan Wasanni – John Enoh
Ministan Abuja – Nyesom Wike
Ministar Al’adu – Hannatu Musawa
Ministan Tsaro – Muhammad Badaru
Ƙaramin Ministan Tsaro – Bello Matawalle
Ƙaramin Ministan Ilimi – Yusuf T. Sununu
Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Ahmed M. Dangiwa
Ƙaramin Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane – Abdullah T. Gwarzo
Ministan Kasafi da Tsare-Tsare – Atiku Bagudu
Ministan Muhalli (Kaduna)
Ƙaramar Ministar Abuja – Mairiga Mahmud
Ministan Albarkatun Ruwa – Bello M. Goronyo
Ministan Noma da Samar da Abinci – Abubakar Kyari
Ministan Ilimi – Tahir Maman
Ministan Harkokin Cikin Gida – Sa’Idu A. Alkali
Ministan Harkokin Waje – Yusuf M. Tuggar
Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a – Ali Pate
Ministan Harkokin ‘Yan Sanda – Ibrahim Geidam
Ƙaramin Ministan Ƙarafa – U. Maigari Ahmadu
Ministan Ƙarafa – Shuaibu A. Audu
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai – Muhammed Idris Malagi
Ministan Shari’a – Lateef Fagbemi
Ministan Ƙwadago da Samar da Ayyuka – Simon B. Lalong
Ƙaramar Ministar Harkokin Cikin Gida – Imaan Sulaiman-Ibrahim
Ministan Ayyuka na Musamman – Zephaniah Jisalo
Ministan Albarkatun Ruwa – Joseph Utsev
Ƙaramin Ministan Noma da Samar da Abinci – Aliyu Sabi Abdullahi