Tinubu ya rattaɓa hannu kan kasafin 2024

Daga BASHIR ISAH   

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya rattaba hannu kan kasafin 2024 na Naira tirilyan 28.7 wanda hakan ya sanya  kasafin zama doka.

A ranar Litinin da ta gabata Tinubu ya sanya wa kasafin hannu da misalin karfe 2:00 na rana a ofishinsa, inda aka shirya kwarya-kwaryar biki wanda ya samu halartar manyan jami’an gwamnatinsa.

Mahalarta bikin sun hada da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio; Shugaban Majalisar Wakilai, Hon Tajudeen Abbas; Ministan Kudi, Mr Wale Edun.

Sauran sun hada da Ministan Kasafi da tsare-tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Atiku Bagudu; Mai bai wa Shugaban Shawara Kan Sha’anin Tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu; Shugaban ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dr Abdullahi Ganduje da dai sauransu.

A ranar Juma’ar da ta gabata ‘yan majalisar tarayya suka yi zama ta hadaka inda a nan suka amince da kasafin wanda hakan ya bai Tinubu damar sanya hannu ya zama doka.