13
Jan
Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawan Tarayyar Nijeriya, Sanata Barau I. Jibrin zai kafa cibiyar horas da jami'an shige da fice ta kasa (NIS) a karamar hukumar Bichi da ke shiyyar jihar Kano ta Arewa. Sanata Barau ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis yayin da Kwanturola-Janar na hukumar NIS, Wuraola Adepoju, ta kai ziyarar ban girma zuwa ofishinsa a majalisar dokokin tarayya dake Abuja. A cikin wata sanarwar manema labarai da mai ba shi shawara akan harkokin yada labarai Ismail Mudashir ya fitar, Sanata Barau ya bayyana yunkurinsa kan samar da cibiyar horaswa ta zamani. “An…
