Editor

9513 Posts
Ma’aikaciyar banki ta kashe kanta saboda ƙuncin rayuwa a Legas

Ma’aikaciyar banki ta kashe kanta saboda ƙuncin rayuwa a Legas

Daga BASHIR ISAH Bayanai daga jihar Legas sun ce, wata ma'akaciyar banki mai suna Amarachi Ugochukwu, ta kashe kanta daboda tsadar rayuwa. Jaridar Intelregion ta rawaito cewa wannan al'amari ya auku ne a ranar Litinin da ta gabata, kuma matar ta kashe kanta ne a cikin bankin da take aiki ta hanyar kwankwadar maganin kashe kwari. An ce da misalin karfe dayan rana na wannan rana ne Ugochukwu ta tafi bandaki inda a nan ta kwankwadi maganain kashe kwari ba tare da abokan aikinta sun sani ba. Daga bisani ne aka ce abokan aikin nata suka fara neman ina ta…
Read More
Tinubu ya sabunta wa NAHCON Kwamitin Gudanarwa

Tinubu ya sabunta wa NAHCON Kwamitin Gudanarwa

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kafa sabon kwamitin gudanawar na Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCOM), kafin lokacin da Majalisar Dattawa za ta tabbatar da nadin. Majiyarmu ta ce Tinubu ya dauki wannan mataki ne domin tabbatar da samun sahihin aikin Hajji kuma mara cunkoso a 2024. Kwamitin zai gudana ne karkashin jagorancin Shugaban NAHCON na Kasa, Jalal Arabi, yayin da sauran mambobin Kwamitin sun hada da: Aliu Abdulrazaq — Commissioner, Policy, Personnel, & Finance Prince Anofi Elegushi — Commissioner, Operations Farfesa Abubakar A. Yagawal — Commissioner, Planning & Research Wakilan Shiyya: Dr. Muhammad Umaru Ndagi — Arewa…
Read More
Ba wani gata da iyaye za su yi wa ‘ya’yansu da ya wuce tarbiyya – Mariya Durumin Iya

Ba wani gata da iyaye za su yi wa ‘ya’yansu da ya wuce tarbiyya – Mariya Durumin Iya

“iyaye su dinga bibiyar ‘ya’yansu mata a gidan aure” Daga AISHA ASAS Mai karatu sannu da jimirin bibiyar shafin Gimbiya. A yau dai da yardar mai kowa da komai za mu kai karshen tattaunawar da muke yi da Mariya Inuwa Durimin Iya, inda za ta fara da amsa tambayar da muka tsaya kanta, kafin sauran tambayoyin su biyo baya. MANHAJA: Wacce shawara ki ke da ita ga iyaye mata kan irin rikon sakainar kashi da suke yi da tarbiyyar 'ya'yansu da sunan zamani? HAJIYA MARIYA: Gaskiya tarbiyyar ‘ya’ya mata tana cikin wani hali da za ka kasa gane shin su…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta ayyana ranar da za ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan Kano

Da Ɗumi-ɗumi: Kotun Ƙoli ta ayyana ranar da za ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan Kano

Kotun Ƙoli ta ayyana Juma'a ta wannan makon a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan shari'ar zaɓen gwamnan Kano da ke gabanta. Sakataren tawagar lauyoyin Jam'iyyar NNPP, Barista Bashir Tudun Wazirci, shi ne ya bayyana haka ga manema labarai. “Gaskiya ne, an tabbatar da hakan a hukumance. Sun faɗa mana mu zo kotu ranar Juma'a don yanke hukunci. "Sun shaida mana kada kowane ɓangare ya zo da lauyoyin da suka wuce biyu," in ji Barista Bashir.
Read More
Nijeriya na buƙatar matashin Shugaban Ƙasa don kawo sauyi – Jikan Sanata

Nijeriya na buƙatar matashin Shugaban Ƙasa don kawo sauyi – Jikan Sanata

Daga AISHA ASAS Tsundumar matasa a harkokin siyasa abu ne mai matukar muhimmanci, domin matasa su ne kashin bayan kowace al'umma, don haka idan sun gyaru, to dukkan kasar ta gyaru. Wakiliyar Blueprint Manhaja, AISHA ASAS, ta samu damar tattaunawa da jajirtaccen matashin da ya jima yana fafutukar wayar da kan matasa kan hanyoyin da za su iya cin gajiyar kurciyarsu ta fuskar siyasa, sannan matashi ne da ya shiga harkar siyasa da kafar dama, kuma ya jima yana cin moriyar ta, tare kuma da janyo matasa ‘yan uwansa don su lashi zumar da ya samu ba tare da kyashi…
Read More
Hazo: NiMET ta gargaɗi masu cutar asma da ma’aikatan jirgin sama

Hazo: NiMET ta gargaɗi masu cutar asma da ma’aikatan jirgin sama

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya, NiMET,  ta ba da sanarwar taka-tsantsan ga masu fama da cutar asma da masu fama da lalurar numfashi da kuma ma'aikatan jirgin sama kan yanayin buji mara kyau da ke tafe. Rahoton da hukumar kula da yanayi ta fitar a ranar Talata ya kuma yi hasashen yanayin zafi da sanyi a jihohin Arewa ta tsakiya na kasar nan daga ranar Laraba 3 ga watan Janairun 2024. "An shawarci mutanen da ke fama da asma da sauran matsalolin numfashi da su yi taka-tsantsan game da yanayin", inji rahoton. "An shawarci ma'aikatan…
Read More
An ƙaddamar da bikin girbin amfanin noma a gonar Daɗin Kowa a Funtuwa

An ƙaddamar da bikin girbin amfanin noma a gonar Daɗin Kowa a Funtuwa

Daga WAKILINMU An kaddamar da bikin cire shinkafa da albarkatun noma na bana a gonar 'Daɗin Kowa Farm’ dake garin Dakamawa a karamar hukumar Funtuwa dake Jihar Katsina. Bikin wanda ya kasance ana aiwatar da shi a karshen damina duk shekara ya kayatar yayin da a ka samu albarkatun noma fiye da na shekarun da suka shude, inda aka samu shinkafa wacce ta fi ta ko'ina yawa da albarka har tan miliyan daya a mashahuriyar gonar ta Daɗin Kowa. Sauran albarkatun noman da aka girbe sun hada da farin wake, masara, gero da dai sauransu. Hajiya Zainab wacce aka fi…
Read More
Betta Edu: ACM ta buƙaci Tinubu ya dakatar da Ministan Cikin Gida, Tunji-Ojo

Betta Edu: ACM ta buƙaci Tinubu ya dakatar da Ministan Cikin Gida, Tunji-Ojo

Ƙungiyar tuntuɓa ta Arewa Consultative Movement (ACM), ta yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan ya dakatar da Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo daga muƙaminsa. Kodinetan ACM na Ƙasa, Kwamred Bilal Galadima, shi ne ya yi wannan kira ranar Laraba a Kaduna. Ƙungiyar Arewa ta yi barazanar haɗa kawunan takwarorinta don shirya zanga-zanga a Kaduna da Abuja ta yadda komai zai tsaya cak muddin Shugaba Tinubu ya ƙi dakatar da Ministan Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo daga kujerarsa. Kwamred Galadima ya ce kamata ya yi a dakatar da Tunji-Ojo "saboda wulaƙanta ofishinsa" kuma daidai da tanadin doka. Ya ce,…
Read More
Kada ku ƙyamaci masu roƙon ku taimaka musu

Kada ku ƙyamaci masu roƙon ku taimaka musu

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Halin kuncin rayuwa da yunwa da ake fama da shi a wannan lokaci na koma bayan tattalin arziki da talauci a kasa, ya jefa iyalai da magidanta da dama cikin wani mawuyacin rayuwa. Samun damar cin abinci sau uku ko sau biyu a wuni ya fara zama tarihi a wajen wasu. Magidanta da dama sun zama marokan karfi da yaji, tun mutum na jin nauyin ya yi roko, har ya fara zama masa jiki, don dai neman abin da zai ciyar da iyali, ko da kuwa shi zai hakura ya kwana da yunwa. Muna sane…
Read More
Gwamna Lawal ya gwangwaje manoma da kayan aiki a Tsafe

Gwamna Lawal ya gwangwaje manoma da kayan aiki a Tsafe

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya raba wa manoman yankin Karamar Hukumar Tsafe kayayyakin aikin gona domin bunkasa harkokin noma a fadin jihar. Rabon kayan aikin wanda ya guda a ranar Litinin, bangare ne na kokarin da gwamnati ke yi wajen farfado da harkokin rayuwa bayan wucewar annobar Korona da kuma shirin tada komadar tattalin arziki daukar nauyin shirin FADAMA III. Mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya ce, Gwamnatin Zamfara ta ware kaso a kasafin 2024 domin gyara madatsan ruwa guda tara da ake da su a yankin Karamar Hukumar Tsafe. Ya kara da cewa, yayin…
Read More