13
Jan
A ranar Laraba da ta gabata, dubban Falasdinawa sun gudanar da wani gangami a Ramallah don nuna adawarsu da ziyarar sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a yankin yayin ziyarar da ya ke kaiwa gabas ta tsakiya dangane da yanqin Isra’ila da zuwa yanzu ya kashe Falasdinawa fiye da dubu ashirin da uku. Galibin Falasdinawan sun rike allunan da ke dauke da rubutun ‘‘ba ma maraba da zuwanka Blinken’’ sun yi dafifi akan tituna gabanin jami’an tsaro su tarwatsa su. Wannan ne ziyara ta biyu da Blinken ke kaiwa gabas ta tsakiya tun bayan faro yaqin na Isra’ila a Gaza…
