Editor

9513 Posts
Yadda rikita-rikitar digiri ɗan jabu ta ruɗa Nijeriya

Yadda rikita-rikitar digiri ɗan jabu ta ruɗa Nijeriya

*Badaqalar ta shafi jami’o’i 78 *An cafke jami’ai bisa zargin hannunsu *Hukumar NYSC ta farga Daga MAHDI M. MUHAMMAD A farkon makon nan ne Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta dakatar da amincewa da takardar shaidar digiri daga wasu jami’o’in kasashen waje da ma masu cibiya a cikin gida. Umarnin na qunshe ne a cikin wata sanarwa ne da aka fitar a ranar Talata, 2 ga Janairu, 2023, mai dauke da sa hannun Augustina Obilor-Duru a madadin Daraktan Yada Labarai Da Hulda Da Jama’a Na Ma’aikatar Ilimi Ta Tarayya. Gwamnati ta koka da cewa "wasu 'yan Nijeriya suna amfani da hanyoyin da…
Read More
Zargin karkatar da N585m:  Tinubu ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan Betta Edu

Zargin karkatar da N585m:  Tinubu ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan Betta Edu

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kasa Bola Tinubu ya ba da umarnin a binciki Ministan Jinkai da Yaki da Talauci, Dokta Betta Edu, dangane da karkatar da Naira miliyan 585 da aka ware don ba da tallafin rage radadin rayuwa zuwa wani kebabben asusu. Bayanin haka na kunshe ne cikin sanarwar da Ministan Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya fitar a ranar Lahadi. A cewar Idris, “Gwamnatin Tarayya, karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na aiki ne da gaskiya ga jama’a tare da tabbatar da an zuba kudaden gwamnati a inda ya dace don magance matsalolin bukatun ‘yan Nijeriya. “Duba…
Read More
Gwamna Lawal ya ƙaddamar da rabon kayan aiki ga manoma a Zamfara

Gwamna Lawal ya ƙaddamar da rabon kayan aiki ga manoma a Zamfara

*Za a gina makarantu tsangaya a mazabun sanata Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya kaddamar da raba kayayyakin aiki ga manoma a shiyyar Zamfara ta Yamma. Shirin wanda ke mazaunin bangare na tayar da komadar da annobar Korona ta haddasa wa Nijeriya da kuma yaukaka tattalin arziki karkashin Shirin FADAMA III, an kaddamar da shi ne a yankin Karamar Hukumar Gummi da ke jihar. Mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar cewa, Gwamna Lawal ya kaddamar da shirin rabon kayayyakin ne hadi da gina Makarantar Tsangaya irin ta…
Read More
‘Yan bindiga sun halaka ‘yan kasuwa takwas a Katsina

‘Yan bindiga sun halaka ‘yan kasuwa takwas a Katsina

Daga Umar Garba a Katsina ‘Yan bindiga masu tarin yawa dauke da muggan makamai sun tare ayarin motocin 'yan kasuwa inda suka kashe wasu mutane takwas a lokacin da suka kai wani hari kan ayarin da ke dawowa daga kasuwar garin Yantumaki da ke karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina. A duk mako 'yan kasuwar kan yi ayari don tafiya cin kasuwa inda suke samun rakiyar jami'an tsaro, sai dai a wannan karon 'yan ta'addar sun yi wa jami'an tsaron kwanton bauna inda suka jikkata wasu daga ciki suka halaka wasu 'yan kasuwar.  Shugaban kungiyar direbobi a yankin, Kabiru Dangaye,…
Read More
Almundahana: Yadda EFCC ke ƙoƙarin titsiye tsofaffin jami’an Buhari mata

Almundahana: Yadda EFCC ke ƙoƙarin titsiye tsofaffin jami’an Buhari mata

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A cikin makon nan ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Shugabar Hukumar Shirin Bada Tallafi da Dogaro da Kai, wato ‘National Social Investment Programme Agency’ (NSIPA), inda a gefe guda kuma tun a makon jiya Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta'annati ta mika goron gayyatarta ga tsohuwar Ministar Jinkai da Agaji a lokacin tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, wato Sadiya Farouq kan zargin ta da hannu a badakalar Naira biliyan 37.1. A bangaren Halima Shehu ta hukuma NSIPA, wacce ke karkashin Ma’aikatar Jinkan, bayanai sun ce hukumar…
Read More
Akwai buƙatar kowa ya sa hannu wajen farfaɗo da ilimin firamare a Zariya – Dr. Hassana

Akwai buƙatar kowa ya sa hannu wajen farfaɗo da ilimin firamare a Zariya – Dr. Hassana

Daga ISAH GIDAN ƁAKKO a Zariya Sakatariyar Ilimi ta Karamar Hukumar Zariya, Dokta Hassana Muhammad Lawal ta bayyana kudurinta na bin duk hanyoyin da su ka dace domin kawo karshen matsalolin da suke addabar makarantun firamare a karamar hukumar Zariya. Dr. Hassana Lawal ta bayyana haka ne a jawabin da ta yi a lokacin dora dambar makarantun firamare da suke qaramar hukumar Zariya, inda ta fara da makarantar firamare ta Zage-zagi a birnin Zariya. Dr. Hassana ta bankado matsalolin da su ke addabar makarantun firare a karamar hukumar Zariya da suka hada da gine-ginen gidaje da sauran gine-gine da al'umma…
Read More
Iyalan da ‘yan bindiga suka kashe sun samu taimakon gwamnatin Katsina

Iyalan da ‘yan bindiga suka kashe sun samu taimakon gwamnatin Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnatin Jihar Katsina ta kashe Naira miliyan 120 wajen tallafa wa iyalan da 'yan bindiga suka kashe a jihar.                                                        Mai ba gwamna shawara akan 'yan gudun hijira Sa'idu Ibrahim Danja wanda ya sanar da haka ya ce wannan kudi an yi amfani da su ne wajen tallafawa marayu da aka kashi masu iyaye sanadiyyar hare-hare na 'yan bindiga a jihar. Mai ba gwamnan shawara ya sanar da haka ne a wata liyafar da wasu aminansa suka shirya masa a Katsina.                                                   Ya ce wannan tallafi da gwamnti ta bada zai taimaka marayun wajen rage masu radadin…
Read More
Emefiele: EFCC ta kai wa Ɗangote sumame bayan rikitowarsa a matsayin attajirin Afirka

Emefiele: EFCC ta kai wa Ɗangote sumame bayan rikitowarsa a matsayin attajirin Afirka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jami’an Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati, EFCC, a ranar Alhamis, sun kai samame babban ofishin Kamfanin Dangote dake Legas. Kamar yadda shafin jaridar TheCable ya rawaito, jami’an hukumar sun gudanar da bincike kan kudaden da aka ware wa kamfanin a zamanin Godwin Emefiele, tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya CBN. Amma Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya qi cewa komai kan batun. Sai dai wani ma’aikacin Kamfanin Dangote ya tabbatar da cewa, jami’an EFCC na nan a babban ofishin kamfanin. “Sun bukaci a ba su takardu kan hada-hadar kudi da CBN,” inji ma’aikacin.…
Read More
Za mu noma hekta 500,000 don bunƙasa abinci da sauƙaƙa shi a Nijeriya -Tinubu

Za mu noma hekta 500,000 don bunƙasa abinci da sauƙaƙa shi a Nijeriya -Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta noma hekta 500,000 domin bunkasawa, wadatarwa da saukaka kayan abinci a fadin Nijeriya. Tinubu bayyana haka a cikin jawabin sa na murnar shiga sabuwar shekarar 2024, wanda ya yi a safiyar Litinin. “Za mu noma hekta 500,000 a fadin kasar nan domin samun masara, shinkafa, alkama, gero da sauran kayan abincin da zai wadaci ‘yan Nijeriya,” inji Tinubu. Cikin watan Nuwamba ne dai Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da shirin noman alkama a Jihar Jigawa, shirin da manoma 250,000 za su ci gajiyar noman alkama a…
Read More
Masu zanga-zanga sun ƙona gidan basarake a Filato

Masu zanga-zanga sun ƙona gidan basarake a Filato

Daga BASHIR ISAH Wasu mata masu zanga-zanga sun kona gidan Dagacin Bokkos, Michal Monday Adanchi, da ke yankin Karamar Hukumar a Jihar Filato. MAHAJA ta kalato cewar, lamarin ya faru ne da tsakar daren ranar Alhamis da misalin karfe 12:30am. Majiyarmu ta ce matan sun kona gidan basaraken ne biyo bayan tsare wasu ‘yan kauyen da aka yi bisa zarginsu da hannu cikin kashe-kashen da ya auku a yankin a baya-bayan nan. A cewar majiyar, “Lamarin ya faro a ofishin ‘yansanda inda matan suka nuna fushinsu dangane da tsare wasu ‘yan uwansu da aka yi. “Bayan da suka baro ofishin…
Read More