Editor

9513 Posts
NAHCON ta tsawaita wa’adin rufe karɓar kuɗin aikin Hajji na 2024

NAHCON ta tsawaita wa’adin rufe karɓar kuɗin aikin Hajji na 2024

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hukumar Alhazai ta Kasa, NAHCON, ta sanar da tsawaita wa’adin rufe karbar kudaden aikin Hajjin bana. A wata sanarwa da mataimakiyar daraktan sashin hulda da jama’a, Fatima Sanda Usara ta fitar a ranar Talata, NAHCON, ta dage wa’adin zuwa 31 ga watan Janairu. Ta ce karin wa’adin ya biyo bayan koke-koken da malaman addini da hukumomin jin dadin alhazai na jihohi, gwamnonin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki kan a tsawaita wa’adin. A cewar Usara, duba da kiraye-kirayen da dumbin al’umma suka yi kan tsawaita wa’adin ya nuna bukatar samar da dama ga…
Read More
2024: Tinubu ya yi alƙawarin wadata Nijeriya da wutar lantarki

2024: Tinubu ya yi alƙawarin wadata Nijeriya da wutar lantarki

 Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya yo alkawarin cewa sabuwar kwangilar da aka rattaba tsakanin Gwamnatin Nijeriya da kamfanin Siemes Energy na Jamus, zai gaggauta samar da wadatacciyar wutar da aka dade fiye da shekaru talatin ana mafarkin samu, amma hakan ya gagara. Shugaba Tinubu ya bayyana hakan a cikin jawabin murnar shiga sabuwar shekarar 2024 da ya yi a safiyar Litinin. “A lokacin Taron COP28 a Dubai, Shugaban Jamus Olaf Scholz da ni mun amince mu gaggauta shirin samar Siemens Energy Power na aikin samar da wadatacciyar wutar lantarki a fadin Nijeriya, wanda aka fara…
Read More
Yadda Kirista ya ɓoye wata Musulma ta haifa masa yara uku a Zariya – Kwamandan Hizbah

Yadda Kirista ya ɓoye wata Musulma ta haifa masa yara uku a Zariya – Kwamandan Hizbah

Daga ISAH GIDAN BAKKO a Zariya Rundunar tsaro ta Hizbah a Karamar Hukumar Sabongarin Zariya a Jihar Kaduna ta samu nasarar cafke wani Kirista da ya boye wata yarinya Musulma na tsawon shekara bakwai. Babban kwamandan Hizbah a karamar hukumar Sabongari, Alhaji Abubakar Auwal Adam ya shaida wa wakilinmu haka a lokacin da ya zanta da shi a cibiyar karamar hukumar Sabongari da ke Dogarawa. Alhaji Abubakar Auwal ya ci gaba da cewar, sun samu nasarar damke mutumin ne mai suna Mista Joe bayan sun dauki dogon lokaci suna gudanar da bincike bisa rahoton sirrin da su ka samu daga…
Read More
Rundunar sojin ruwa ta miƙa buhunan tabar wiwi da ta ƙwato ga NDLEA

Rundunar sojin ruwa ta miƙa buhunan tabar wiwi da ta ƙwato ga NDLEA

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A ranar Talata ne rundunar sojin ruwan Nijeriya a Badagry a Legas, ta mika buhunan tabar wiwi guda takwas da kudinsu ya kai Naira miliyan 12.8 ga hukumar yaqi da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA a Badagry. Laftanar Adedeji Adeyemi, Kwamandan Tsaro na cikin gida mai wakiltar bataliyar FOB, Commodore Aiwuyor Adams-Aliu, ya ce jami’an sojin ruwa sun kama abinda ake zargin tabar wiwi ne a ranar Litinin a unguwar Abojedo da ke kusa da gavar tekun Sultan, a Badagry. A cewar Mista Adeyemi, bataliyar ta FOB, ta yi aiki ne…
Read More
2024: Tinubu ya jaddada aniyar yi wa ma’aikata sabon tsarin albashi

2024: Tinubu ya jaddada aniyar yi wa ma’aikata sabon tsarin albashi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin yi wa ma’aikata karin albashi ta hanyar sake tsarin mafi kankantar albashin ma’aikatan gwamnatin tarayya. Gwamnatin Tarayya za ta yi hakan ne bisa yin la’akari da tsadar rayuwar da ake fuskanta a fadin kasar nan. Shugaba Tinubu ya bayyana haka a ranar Litinin, a cikin jawabin murnar shiga sabuwar shekarar 2024. Ya ce za a qara albashin ne domin kowane dan Nijeriya ya ji a jikinsa cewa gwamnati ta na kula da halin da ya ke ciki, musamman marasa galihu, talakawa da fakirai da matsakaitan karfin tafiyar da…
Read More
Gwamnatin Kano za ta haɗa gwiwa da masu hannu da shuni wajen tallafa wa ilimi

Gwamnatin Kano za ta haɗa gwiwa da masu hannu da shuni wajen tallafa wa ilimi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano ta ce ta kammala shirye-shiryen hadin gwiwa da masu hannu da shuni wajen daukar nauyin harkar ilimi a jihar. Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka ne a lokacin da ya karvi bakuncin shugabannin gidajen yada labarai a ofishinsa a ranar Talata a Kano. Ya ce matakin na daga cikin matakan bunkasa fannin ilimi, wanda tun daga hawan gwamnatinsa, ta sanya dokar tabaci. Ya kara da cewa, “ba za mu iya tallafa wa ilimi mu kadai ba sai da taimakon masu hannu da shuni, don haka akwai bukatar mu hada hannu…
Read More
Ba abin da ya fi a rayuwar mace kamar ɗora ta kan hanyar ilimi – Mariya Durumin Iya

Ba abin da ya fi a rayuwar mace kamar ɗora ta kan hanyar ilimi – Mariya Durumin Iya

"Mace na rayuwa ne ƙarƙashin kulawar wasu har ƙarshen rayuwarta" Ci gaba daga makon jiya Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, mun fara shimfida kan tattaunawar da muke yi da daya daga cikin matan Arewa da suke da gidauniyar taimakon al'umma, inda muka soma da jin tarihin rayuwarta, yadda ta fara tunanin bude wannan gidauniyar da kuma hanyoyin da ta bi har hakarta ta cimma ruwa. A wannan sati, za mu soma ne da samar wa masu karatu amsar tambayar da muka kwana kanta, kamar yadda muka yi alkawari, kafi wasu tambayoyin su biyo baya. Har wa yau…
Read More
‘Yan bindiga sun sako Shugaban Karamar Hukumar Akwanga bayan biyan kuɗin fansa

‘Yan bindiga sun sako Shugaban Karamar Hukumar Akwanga bayan biyan kuɗin fansa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Karamar Hukunar  Akwanga a Jihar Nasarawa, Safiyanu Isah Andaha, ya shaƙi iskar 'yanci bayan da 'yan bindiga suka yi garkuwa da shi. An sako shi ne tare da  abokinsa, Adamu Custom da wasu mutum biyu wadanda aka yi garkuwa da su a lokaci guda ranar Litinin da daddare. MANHAJA ta kalato cewa, sai da aka biya fansar Naira miliyan 10 kafin aka sako wadanda lamarin ya shafa. Majiya da ta bukaci a dakaya sunanta ta bayyana cewa, an saki wadanda aka yi garkuwa da su din ne a bayan wani gidan mai da ke hanyar Bayan…
Read More
Gwamnati ta yi watsi da shirin karin kudin wutar lantarki

Gwamnati ta yi watsi da shirin karin kudin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta yi tsayin daka kan kin amicewa da karin farashin wutar lantarki kamar yadda kamfanin samar da lantarki na Nijeriya ya bukata. Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin. Ministan ya jaddada kudurin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da wadatacciyar wutar lantarki a kasa. Adelabu ya kara da cewa, “Rashin damarmaki na ci gaba da zama babban kalubalen da fannin lantarki ke fuskanta. “Muna yin nazari kan tsarin aiwatar da jadawalin kuɗin fito tare da tabbatar da ci…
Read More
2023: Shekarar sace ’yan makaranta da tsadar rayuwa

2023: Shekarar sace ’yan makaranta da tsadar rayuwa

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Wannan mako shi ne na karshe cikin wannan shekara ta Miladiyya ta 2023, ga masu nisan kwana. Cikin yardar Allah mai kowa mai komai, mun kasance cikin masu rai da lafiya da suka ga wannan shekara. Da fatan Allah zai ja kwanakinmu mu ga shekara mai zuwa cikin rayayyu. Abubuwa da dama sun faru da za su dade a zukatan ’yan Nijeriya, na dadi da akasin haka, wadanda za a yi ta tunawa da su, saboda tasirinsu a rayuwarmu. Kama daga shirye-shiryen Babban Zaven 2023 da kafa sabuwar gwamnati, cire tallafin man fetur, tsadar rayuwa, hukuncin…
Read More