22
Dec
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed ya jaddada aniyarsa ta yi wa kowa adalci a mulkinsa tare da tabbatar da ya haɗa kan 'yan Nijeriya da samar da walwala ga ƙasar da 'ya'yanta. Da yake jawabi bayan kammala sallar Juma'a a babban masallacin Ansar-Ud-Deen da ke Suruleren, Jihar Legas, a ranar Juma’a, Shugaban ya ce sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnatinsa ta ɓullo da su na da nufin samar da tsayayyen tushe da 'ya'ya da jikokin 'yan Nijeriya za su mora. Shugaba Tinubu, wanda ya bi sahun al’ummar Musulmi wajen gudanar da addu'o'in bikin cikar ƙungiyar Musulmi ta Ansar-Ud-Deen Society of Nigeria shekara…
