03
Dec
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Cikin makon da ya gabata ne Kwamishinan harkokin cikin gida da tsaro na jihar Neja, Manjo Janar Bello Mohammed Abdullahi (mai ritaya) ya ci zarafi, tare da tozarta wakilin gidan Radiyon Muryar Amirka na jihar Neja, Alhaji Mustapha Nasiru Batsari. Da ya ke nuna takaicin sa game da wannan lamari, Shugaban Ƙungiyar 'yan jarida ta qasa NUJ, reshen jihar Neja, Kwamared Abu Nmadu ya bayyana wannan abu a matsayin abin takaici. Abu Nmadu ya ci gaba da cewa sun kaɗu matuƙa da jin faruwar wannan lamari, wanda ya ce ba za su tava lamuntar irin wannan…
