Editor

9513 Posts
Mun ƙara himmar kula da matan da suka tsira daga cin zarafi bisa tallafin shirin Tarayyar Turai da Majalisar Ɗinkin Duniya – Gwamna Aliyu

Mun ƙara himmar kula da matan da suka tsira daga cin zarafi bisa tallafin shirin Tarayyar Turai da Majalisar Ɗinkin Duniya – Gwamna Aliyu

Yayin da aka kammala aikin shirin kawo karshen cin zarafin mata na Ƙungiyar Tarayya Turai (EU) da Majalisar Dinkin Duniya tare da mikawa ga masu ruwa da tsaki, Gwamnan Jihar Sokoto, Dr Ahmed Aliyu, ya bayyana cewa bisa tallafin shirin, gwamnatin jihar ta inganta kula da waɗanda suka tsira daga Cin Zarafi na Jinsi (SGBV) a cikin jihar. "Mun inganta ayyukan kula da waɗanda suka tsira daga cin zarafi na Jima'i saboda bambancin jinsi (SGBV) kuma mun tabbatar da cewa mata da 'yan mata sun sami damar samun kulawar da suke buƙata don sake gina rayuwarsu." Ya bayyana hakan ne…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: INEC ta ayyana Uzodinma a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna a Imo

Da Ɗumi-ɗumi: INEC ta ayyana Uzodinma a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna a Imo

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana ɗan takarar gwamna na Jam'iyyar APC a Jihar, Hope Uzodimma, a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan da ya gudana a jihar a ranar Asabar da ta gabata. A cewar baturen zaɓen da ya jagoranci tattara sakamakon zaɓen, Abayomi Fasina, Uzodimma ya lashe zaɓen ne da ƙuri' 540,308. Yayin da ɗan takarar Jam'iyyar PDP, Sanata Samuel Anyanwu, ya rufa masa baya da ƙuri'u 71,503. Ɗan takarar Jam'iyyar LP, Sanata Athan Achonu ne ya zo na uku a zaɓen inda ya tsira da ƙuri'u 64, 081.
Read More
Hukumar jin daɗin Alhazai ta jihar Kebbi ta bai wa maniyyata wa’adin sati biyu

Hukumar jin daɗin Alhazai ta jihar Kebbi ta bai wa maniyyata wa’adin sati biyu

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Hukumar Jin Daɗin Alhazzai ta Jihar Kebbi qƙarƙashin jagoranacin Alhaji Faruk Musa Yaro ta bai wa maniyyata wa'adin sati biyu da su kammala biyan kuɗin kujera. Ya yi wannan bayanin ne a yayin wata ganawa ya yi da shuwagabannin ƙananan hukumomi ashirin da ɗaya da ke jihar. Alhaji Faruk Musa ya bayyana wa shuwagabannin ƙananan hukumomin irin ƙoƙarin da hukumar ke yi na ganin an samu ingantaccen aikin Hajji da za a gudanar a shekarar 2024 mai zuwa. Shugaban hukumar ya bayyana cewa ya zama wajibi ga dukkan maniyyaci ya gaggauta biyan kuɗin kujerarsa kafin…
Read More
‘Yan Nijeriya za su fara bin diddigin ayyukan da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa – Minista

‘Yan Nijeriya za su fara bin diddigin ayyukan da Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa – Minista

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kwanan nan ‘yan Nijeriya za su samu damar iya bibiya da sa ido kan ayyukan raya ƙasa waɗanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa. Ministan ya bayyana haka a lokacin da ya ke ganawa da editocin wasu jaridu a ranar Litinin, a Abuja. A yayin ganawar, Idris ya ce, “Shugaban Ƙasa ya bada umarnin a yi amfani da fasahar zamani domin bai wa ‘yan Nijeriya damar sa ido, bibiya da bin diddigin ayyukan raya qasa waɗanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa a faɗin ƙasar…
Read More
Dattawan Arewa sun nuna damuwa kan rikicin Ɗangote da BUA

Dattawan Arewa sun nuna damuwa kan rikicin Ɗangote da BUA

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana damuwarta kan rashin jituwar da ke faruwa tsakanin tsohon Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Matawalle da Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, inda suka yi kira ga ‘yan siyasar da su rungumi zaman lafiya. NEF ta kuma ce ta damu da yaƙin sunƙuru tsakanin fitattun ‘yan kasuwar Arewacin Nijeriya, Alhaji Aliko Ɗangote da Abdussamad Rabiu na kamfanin BUA. Dattawan Arewa sun yi zargin cewa wannan faɗan yana shafar tattalin arziki da siyasar yankin. A cewar NEF rikicin da ake fama da shi a yanzu tsakanin Aliko Ɗangote da Abdussamad…
Read More
Jarumi Samanja ya kwanta dama

Jarumi Samanja ya kwanta dama

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa jarumin wasan Hausa, Usman Baba Fategi da aka fi sani da Samanja, rasuwa. Majiyarmu ta ce, Samanja ya rasu ne da safiyar wannan Lahadin a wani asibitin Kaduna bayan fama da rashin lafiya. Duk da dai iyalan marigayin ba su fitar da wata sanarwa ba dangane da rasuwar tasa, amma MANHAJA ta kalato cewa a wannan Lahadin za a yi jana'izar marigayin. Marigayin ya bar dunya yana da shekara 81, kuma ya rasu ya bar mata biyu da 'ya'ya 14. Samanja tsohon soja ne inda daga bisani ya kama aiki da Rediyon Tarayya…
Read More
Raɗɗa ya yi Allah-wadai da kashe mutane 20 da ‘yan bindiga suka yi wajen taron mauludi a Katsina

Raɗɗa ya yi Allah-wadai da kashe mutane 20 da ‘yan bindiga suka yi wajen taron mauludi a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Gwamnan jihar Katsina Dikko Umar Raɗɗa ya yi Allah-wadai da hallaka mutane 20 da wasu 'yan bindiga su ka yi a Ƙaramar Hukumar Musawa ta jihar Katsina lokacin da suke gudanar da taron Mauludi. Kazalika, gwamnan ya kuma jajentawa al'ummar ƙaramar hukumar Matazu dangane da kashe mutane biyar da wasu 'yan bindigar su ka yi a wani harin na daban. Raɗɗa ya bayyana haka ne a ƙaramar hukumar Musawa lokacin da ya kai ziyarar ta'aziya ga iyalan waɗanda 'yan bindigar suka kashe a hare-haren da su kai a ƙananan hukumomin Musawa, Ɗan Musa, Matazu da…
Read More
Farfesa a ABU ya maido Naira miliyan 1 da aka biya shi bisa kuskure

Farfesa a ABU ya maido Naira miliyan 1 da aka biya shi bisa kuskure

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban makarantar horas da sojoji NDA John-Ochefu Ochai a ranar Laraba ya ziyarci Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) dake Zariya domin ganawa da Farfesa Umar Ka’oje bayan ya maido da sama da Naira miliyan 1 da aka biya shi bisa kuskure. Kuɗaɗen da aka biya farfesan sun kai Naira miliyan 1,153,953.36. Waɗannan kuɗaɗen na aikin karantarwa da ya yi ne a NDA aka biya shi haƙƙinsa. Ochai ya zo Jami’ar tare da wasiƙa godiya da yabo daga NDA wacce ke ɗauke da kwanakin wata 12 ga Satumba, 2023. Shugabar sashen koyar da kwas ɗin ‘Political…
Read More
Matar gwamnan Kebbi za ta haɗa gwiwa da Intel Box don haɓɓaka ayyukan SDGs

Matar gwamnan Kebbi za ta haɗa gwiwa da Intel Box don haɓɓaka ayyukan SDGs

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Matar gwamnan Kebbi Hajiya Zainab Nasir Idris nemi haɗin gwiwa tsakanin Nasara Foundation da Intel Box a kan muradun ƙarni SDGs. Ta yi wannan bayani ne a lokacin da ta kai ziyara a ofishin Intel Box Solution Ltd a Abuja babban Birnin tarayyar Nijeriya ranar Talatar da ta gabata. Ta ce wannan haɗin gwiwar zai yi tasiri wajen inganta rayuwar al'umma ta fannoni da yawa da suka haɗa da ilmin 'ya'ya mata, horas da makamai kiwon lafiya, mata masu ciki da jinjirai da kuma koyar da sana'o'in hannu ga mata da matasa. Ta ƙara…
Read More
Ba mu bayar da umarnin janye tsofaffin takardun kuɗin Naira ba – CBN

Ba mu bayar da umarnin janye tsofaffin takardun kuɗin Naira ba – CBN

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya ce duk takardun kuɗi (tsofaffi da sababbi) suna nan a kan doka. Wannan na zuwa ne sakamakon fargabar da ake ciki cewa tsofaffin takardun kuɗi za su daina aiki nan da watan Disamba 2023. Wata sanarwar da mai magana da yawun bankin CBN, Isah Abdulmunin ya fitar a ranar Laraba, ta ce bankin bai bayar da umarnin janye tsofaffin takardun kuɗi ba daga wajen al'umma. Bankin ya ce, “An kuma samu rahotannin damuwa da wasu jama’a ke nunawa kan halacci ko rashinsa na tsoffin takardun kuɗin Naira. “Don kauce wa shakku,…
Read More