Editor

9513 Posts
Wata ƙungiyar Jam’iyyar ANPP da masu ruwa da tsaki sun buƙaci a mara wa Tinubu baya

Wata ƙungiyar Jam’iyyar ANPP da masu ruwa da tsaki sun buƙaci a mara wa Tinubu baya

Daga BASHIR ISAH Wata ƙungiya ta mabobin Jam'iyyar ANPP tare da tawagar masu ruwa da tsaki sun buƙaci 'yan Nijeriya da su bai wa Shugaba Bola Ahmad Tinubu da gwamnatinsa cikakken goyon baya don cigaban ƙasa. Ƙungiyar ta buƙaci hakan ne cikin sanarwar da ta fitar a Abuja mai ɗauke da sa-hannun shugabanta, Malam Kabiru Muhammad Gwangwazo. Da yake tsokaci kan nasarar da Tinubu ya samu a Kotun Ƙoli, Muhammad wanda tsohon shugaban ANPP ne a Jihar Kano, ya yi kira ga ɗaukacin masu ruwa da tsaki da su rufa wa Tinubu da gwamnatinsa baya don amfanin ƙasa. Ya ce,…
Read More
Buhari ya taya jam’iyyar APC murnar lashe zaɓen gwamna a jihohin Imo da Kogi

Buhari ya taya jam’iyyar APC murnar lashe zaɓen gwamna a jihohin Imo da Kogi

Daga UMAR GARBA a Katsina Tsohon shugaban ƙasar Nijeriya Muhammadu Buhari, ya ta ya jam'iyyarsa ta APC murnar lashe zaɓukan gwamna da hukumar zav'ɓe mai zaman kanta ta gudanar a ranar Asabar da ta gabata. Buhari ya gode wa al'umar jihohin biyu bisa amincewa da sake ba wa jam'iyyar ta APC dama a jihohin. Tsohon shugaban ƙasar ya kuma gode wa shugabannin jam'iyya da kuma ma'aikata wax'ɗanda su ka yi aiki ba dare ba rana don tabbatar da sake zaɓen Hope Uzodimma na jihar Imo da kuma Usman Ododo a matsayin sabon Gwamnan Jihar Kogi. Daga ƙarshe, Buhari ya yi…
Read More
Zaɓen Bayelsa: Gwamna Diri ya yi ta-zarce

Zaɓen Bayelsa: Gwamna Diri ya yi ta-zarce

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana ɗan takarar Jam'iyyar PDP, Gwamna Douye Diri, a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamna a jihar Bayelsa. Da wannan, Diri ya samu yin ta-zarce ke nan inda zai cigaba da shugabancin jihar nan da shekaru huɗu masu zuwa. Diri ya lashe zaɓen ne da ƙuri'u 175,196, sannan ɗan takarar Jam'iyyar APC, Sylva, ya rufa masa baya da ƙuri'u 110,108. Sai kuma ɗan takarar Jam'iyyar LP wanda ya zo na uku da ƙuri' 905.
Read More
Sama da mutum 30 sun mutu a hatsarin jirgin ruwa a Taraba

Sama da mutum 30 sun mutu a hatsarin jirgin ruwa a Taraba

Daga BASHIR ISAH Aƙalla mutum 32, ciki har da ƙananan yara su 20 da iyaye 12 ne suka riga mu gidan gaskiya sakamakon hatsarin jirgin ruwan da ya ritsa da su a garin Ibbi, cikin Ƙaramar Hukumar Ibbi a Jihar Taraba. Bayanai sun ce jirgin da ya yi hatsarin ya yiwo jigilar masunta su sama da 50 daga Ibbi da nufin zuwa gabashin Nijeriya. Hatsarin wanda ya auku a ranar Asabar, ya faru ne a kusa da Zabu da ke iyakar Taraba da Binuwai a Kogin Binuwai. News Point Nigeria ta rawaito wani mazaunin garin Ibbi, Malam Ibrahim Ibbi, ya…
Read More
WAEC za ta fara amfani da tsarin rubuta jarrabawa na ‘CBT’

WAEC za ta fara amfani da tsarin rubuta jarrabawa na ‘CBT’

Daga BASHIR ISAH Hukumar Shirya Jarrabawa ta Afirka ta Yamma (WAEC), ta bayyana cewa, nan ba da jimawa ba za ta fara amfani da tsarin rubuta jarraba ta yin amfani da kwamfuta wanda aka fi sani da CBT a taƙaice, ga ɗalibai masu zaman kansu da za su yi rijista a ƙarƙashinta. Sanarwar da sashen hulɗa da jama'a na WAEC ya fitar mai ɗauke da sa-hannun babban jami'in hukumar, Moyosola F. Adesina a Yaba, Legas, ta ce ya zuwa ranar Litinin, 18 ga Disamban 2023 za ta fara yi wa mabuƙata rijista. Sanarwar ta nuna hukumar za ta fara amfani…
Read More
Makamashi: Matatun man fetur a ƙasa

Makamashi: Matatun man fetur a ƙasa

Tare da BASHIR MUDI YAKASAI A kullum manazarta da masana al’amuran yau da kullum za ka ji hikimomi a lafuzansu, kamar da suke cewa, “mai uwa a gindin murhu…”, suka ce, “ba zai ci tuwansa gaya ba,” wato ba miya. Amma abin takaici a Nijeriya da muke da rijiyoyin man fetur sama da 100 da suke fitar da ɗanyen man fetur fiye da ganga milliyan biyu a kullum, amma matatun man fetur na ƙasa ba sa aiki sama da shekaru 10, kuma babu wani dalili tartibun na rashin aikin nasu. Idan muka bi tarihin kakkafa matatun makamashin man fetur da…
Read More
Jihohin Arewacin Nijeriya suna fuskantar masifar yunwa

Jihohin Arewacin Nijeriya suna fuskantar masifar yunwa

Jihohin Katsina, Zamfara, Borno, Kano, Kaduna, Yobe, Nasarawa da Katsina kusan mutane miliyan 20 suna fuskantar qarancin abinci saboda janye tallafin mai da gwamnatin da ta gabata ta assasa sabuwar gwamnatin Tinubu kuma ta aiwatar. Lamarin ya sa mutane ba sa iya sayen abinci su ci saboda matsanancin talauci da rashin tsaro ya haifar. Dokta Abubakar Sulaiman mataimakin shugaban hukumar samar da abinci da bunƙasa noma na Majalisar Ɗinkin duniya shi ne ya bayyana haka cikin hirarsa da BBC. Inda ya ce, janye tallafin mai ya sa matuƙar ana son mutane su rayu dole a ba su kuɗin sayen abinci…
Read More
Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

Matsalar matsananciyar yunwa a Nijeriya

An yi hasashen cewa 'yan Nijeriya miliyan 25 na iya fuskantar matsananciyar yunwa tsakanin watan Yuni zuwa Disambar 2023 idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba don magance matsalar. Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nakalto Cadre Harmonise a watan Oktoba na shekarar 2022, wani bincike na abinci mai gina jiki ƙarƙashin jagorancin gwamnati da Majalisar Ɗinkin Duniya, yana mai nuni da cewa an yi hasashen cewa alƙaluman na ƙaruwa daga sama da mutane miliyan 17 da ke fuskantar barazanar ƙarancin abinci a halin yanzu a ƙasar. A cikin wannan adadi, mutane miliyan uku suna…
Read More
Zaɓen Gwamnan Kogi: INEC ta bayyana lokacin da za ta sake zaɓe a wasu mazaɓu

Zaɓen Gwamnan Kogi: INEC ta bayyana lokacin da za ta sake zaɓe a wasu mazaɓu

Daga BASHIR ISAH Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce ya zuwa ranar Asabar mai zuwa za ta sake zaɓe a wasu mazaɓu da aka dakatar da zaɓensu yayin zaɓen gwamna a Jihar Kogi. Ta ce za a sake zaɓen ne a unguwanni guda tara da ke mazaɓar sanata ta tsakiya a jihar. Wuraren da aka dakatar da zaɓen suna yankin Ƙaramar Hukumar Ogori/Magongo ne a jihar. Kwamishinan INEC na ƙasa, Mohammed Haruna, ya bayyana a ranar Lahadi cewa, za a sake gudanar da zaɓen a mazaɓun da lamarin ya shafa ne a ranar 18 ga Nuwamba daidai da Sashe…
Read More
Mace Manjo-Janar ta farko a Sojin Nijeriya ta kwanta dama

Mace Manjo-Janar ta farko a Sojin Nijeriya ta kwanta dama

Daga BASHIR ISAH Mace ta farko da ta kai matsayin Manjo-Janar a sojin Nijeriya, Aderonke Kale, ta riga mu gidan gaskiya Rundunar Sojin Nijeriya ta bayyana marigayiyar a matsayin tauraruwa wadda ta nuna ƙwazo da cikakkiyar biyayya a bakin aiki a halin ratuwarta. Rundunar ta ce, ƙwazon da marigayiyar ta nuna a bakin aiki a halin rayuwarta ya bai wa jami'ai da dama samun cigaba a bakin aiki. Cikin sanarwar da ya fitar, Daraktan Hulɗa da Jama'a na rundunar, Brigadier General Onyema Nwachukwu ya ce, “Rundunar Sojin Nijeriya ta samu labarin rasuwar Manjo Janar Aderonke Kale (mai murabus) CFR mni,…
Read More