Editor

9513 Posts
Tarihin Gidan Arewa a Kaduna

Tarihin Gidan Arewa a Kaduna

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gidan tarihi na Arewa (Arewa House Centre For Historical Research and Documentation) da ke garin Kaduna a yankin arewa maso yammacin Nijeriya, cibiya ce da ke tattara tarihin Marigayi Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato da Lardin Arewa da kuma tarihi da al'adu da sana'o'in yankin. An kafa cibiyar ne bayan kisan gillar da aka yi wa Firimiyan Arewa na farko Sardauna, a juyin mulkin da sojoji suka yi a Ranar 15 Ga Watan janairun shekarar alif 1966. Sojojin sun tayar da bam, suka kuma kashe Sardauna da matarsa da ma'aikatansa a wannan gida. A juyin mulkin ne…
Read More
Da Ɗumi-ɗumu: Mun tsare waɗanda suka farmaki Ajaero ku yi haƙuri ku janye yajin aiki, Gwamnati ga NLC

Da Ɗumi-ɗumu: Mun tsare waɗanda suka farmaki Ajaero ku yi haƙuri ku janye yajin aiki, Gwamnati ga NLC

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Taryya ta ce a halin da ake cike ta samu nasarar tsare waɗanda Shugaban NLC na ƙasa, Joe Ajaero, ya ci na-jaki a hannusu, don haka ta ce tana bai wa ƙungiyar haƙuri kan ta dubi Allah ta janye yajin aikin da take yi. Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Sha'anin Tsaro (NSA), Nuhu Ribadu, shi ne ya tabbatar da tsare waɗanda lamarin ya shafa wanda ake zargin 'yan bangan siyasa ne. MANHAJA ta rawaito an farmaki shugaban NLC ɗin ne a Owerri, babban birnin Jihar Imo, a ranar 1 ga Nuwamban 2023, a lokacin…
Read More
CBN ya shure wa’adin daina amfani da tsoffin takardun Naira

CBN ya shure wa’adin daina amfani da tsoffin takardun Naira

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya tsawaita wa'adin amfani da tsaffin takardun Naira, N200, N500 da kuma N1,000 har illa ma sha'a. Daraktan sashen sadarwar bankin, Isa AbdulMumin, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar ranar Talata mai taken, “CBN zai bada damar ci gaba da amfanin da tsaffin takardun Naira a dokance." Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne daidai da yadda hada-hadar kuɗaɗe ke gudana a ƙasashen duniya. Idan za a iya tunawa, a Oktoban 2022 ne CBN ya ƙaddamar da sabbin takardun kuɗi na N200, N500 da N1000, sannan ya yanka…
Read More
Muhimmancin taimako

Muhimmancin taimako

Assalamu alaikum! Godiya ga Allah Maɗaukakin sarki, da ya sake ba ni damar aika wasiƙa ta zuwa ga al’umma, ta wannna jarida (Blueprint Manhaja) mai albarka. A matsayinmu na mutane masu hankali, abu ne da ya kamata kowa ya gane cewa, duk wani ɗan Adam, komai muqaminsa, komai ƙarfin arzikinsa, komai ƙarfin jikinsa, yana buƙatar taimako. Idan ba ya buƙatar tallafin dukiya, to yana buƙatar wani, idan bai buƙatar wani tallafin, to ala tilas ɗinsa, yana da wata buƙatar daga ɗan uwansa mutum. Kamar yadda al’amarin yake, Allah Ya halicci ɗan Adam ne a matsayin mai kasawa, wanda dole ne…
Read More
Siyasar talaka

Siyasar talaka

Tabbas talakawa ne a gidan gaba wajen yin sanadin samun nasara ga duk wani wanda ya fito takara. Talaka ne wanda zai yi siyasa ta a mutu a kan wani ko a kan jam'iyya amma kuma duk da hakan a yi nasara ya zamo an juya mai baya an dafe madafun iko. Tabbas an daɗe a nai ma talakawa alƙawura kamar da gaske wanda idan nasara ta zo sai dai su bar ma Allah haƙƙin su. Ina fatan yan siyasa su riqa kyakkyawar kula cewa ba ka zamaninka kuma kai na wasu idan ma an zave ka ko kuma an…
Read More
Bankin Musulunci zai kashe wa Nijeriya biliyoyin Dala

Bankin Musulunci zai kashe wa Nijeriya biliyoyin Dala

Daga BASHIR ISAH Bankin Bunƙasa Musulunci (UDB) ya shirya zai kashe wa Nijeriya biliyoyin Dalar Amurka domin aiwatar da ayyukan cigaban ƙasa. Mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale ne ya bayyana haka ranar Talata. Ya ce tallafin ɓangare ne na ribar tattaunawar zuba jari da Shugaba Tinubu ya yi da Mataimakin IDB, Dr. Mansur Muhtar, yayin da suka haɗu a Makka, Saudiyya. A cewar Ajuri, yayin tattaunawar tasu, Tinubu ya ce, "Nijeriya fitila ce da za ta haskaka wa sauran ƙasashen Afirka hanya, kuma da zarar Afirka ta ɗau haske, duniya za ta yi wa al'umma daɗin zama."…
Read More
Tinubu ya yi alhinin rasuwar Samanja

Tinubu ya yi alhinin rasuwar Samanja

Shugaban Ƙsa Bola Tinubu ya jajanta wa iyalan tsohon Soja, ma'aikacin yaɗa labarai, kuma fitaccen jarumi, Usman Baba Pategi wanda aka fi sani da Samanja, wanda ya rasu a ranar Lahadin da ta wuce yana da shekaru 84. Shugaban ya bayyana rasuwar fitaccen ɗan wasan a matsayin babban rashi na mutumin da ya bayar da gudunmuwa ga ƙasarsa a duk wata dama da ya samu ta hanyoyi daban-daban. "Marigayi Pategi dan kishin ƙasa ne da ya zaɓi ya amsa kiran ƙasarsa a lokacin da ta ke buƙatar hidimar sa, shirinsa na talbijin, mai taken Samanja, ya ɗebi ɗimbin shekaru a…
Read More
Marubuci ne ke riƙe da fim bakiɗaya – Mubarak Dakta

Marubuci ne ke riƙe da fim bakiɗaya – Mubarak Dakta

"Sai an janyo marubuta jiki, an maIda su mutane ne za a ci moriyar harkar fim" Daga AISHA ASAS  A wannan sati, shafin Nishaɗi na Blueprint Manhaja ya karɓi baƙuncin wani haziƙin matashi, wanda ya samu shuhura a ɓangaren rubutun fim. Matashin, wanda ya ƙware ba a iya rubutun fim ba kaɗai, har ma da na zube, ya bayyana wa Bleprint Manhaja yadda ya fara da kuma finafinan da ya rubuta, kafin ya yi bayani kan muhimmancin marubuci a harkar fim da kuma irin yadda ake tauye marubuci a masana'antar finafinai. Idan kun shirya, Aisha Asas ce tare da Mubarak Idris…
Read More
Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya ta yi jimamin mutuwar abokan aikinta a Gaza

Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya ta yi jimamin mutuwar abokan aikinta a Gaza

Ma'aikatan Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, a ranar 13 ga watan Nuwamba 2023, sun bi sahun takwarorinsu na dukkan tashoshin da ke aiki a duniya domin yin shiru na minti daya domin tunawa da ma'aikatan Majalisar Ɗinkin Duniya da suka rasa rayukansu a yakin da Isra'ila da Hamas ke ci gaba da yi a Gaza. “Yana da matuƙar baƙin ciki cewa muna tare da dukkan jami'an Majalisar Ɗinkin Duniya a duk fadin duniya a dukkan tashoshin da ke aiki don yin shiru na minti daya a yau Litinin, 13 ga watan Nuwamba, 2023 don girmama abokan aikinmu da aka kashe…
Read More
NLC ta tsunduma yajin aiki kan gana wa shugabanta na ƙasa uƙuba

NLC ta tsunduma yajin aiki kan gana wa shugabanta na ƙasa uƙuba

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙwadago ta Ƙasa (NLC) da ta 'yan kasuwa (TUC) sun tsunduma yajin aikin gamagari a ranar Talata. Shiga yajin aikin na da nasaba da uƙubar da aka gana wa shugaban NLC na ƙasa, Joe Ajaero kwanan nan a Jihar Imo, wanda a cewar ƙungiyar hukumomin da lamarin ya sha sun gaza yin komai kan batun. Daga cikin buƙatun da NLC ta nema dangane da haka, har da neman a hukunta da kuma sallamar jami'in ɗan sandan da ya jagoranci lakaɗa wa Ajaero duka. Haka nan, ta nemi a hukunta wani hadimin Gwamna Hope Uzodinma na yin…
Read More