Editor

9513 Posts
Kogi, Imo, Bayelsa: Gobe za a gwada ‘imanin’ gwamnatin Tinubu

Kogi, Imo, Bayelsa: Gobe za a gwada ‘imanin’ gwamnatin Tinubu

•Zaɓen farko tun bayan kafuwar gwamnatinsa Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kimanin masu kaɗa ƙuri’a miliyan 5.2 ne za su fito a ranar 11 ga Nuwamba, 2023 don zaɓen gwamnoni a jihohin Bayelsa, Imo da Kogi. Adedayo Akinwale, ya yi nazari kan matakin shirye-shiryen alƙalan zaɓe, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa. Yayin da zaɓen gwamnan jihar Bayelsa da Kogi da kuma Imo ke ƙara ƙaratowa a ranar 11 ga watan Nuwamba, jimillar mutane 5,409,438 da suka yi rajista a jihohin uku ke shirin zaɓar sabbin shugabannin zartarwa na jihohin uku. Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa…
Read More
Gwamna Dauda: Saboda ya zama izina nake tona asirin Matawalle

Gwamna Dauda: Saboda ya zama izina nake tona asirin Matawalle

*Ya sake zargin shi da wawure biliyan N1 don guraren shaƙatawa Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnan Jihar Zamfara a ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal Dare ta bayyana cewa, ba yana yin tone-tone ga gwamnan da ya gada, Muhammad Bello, Matawallen Muradun, ba ne, don kawai yana sa sha’awar ya tozarta shi, illa don ya zama izina ga duk wanda aka ɗora amanar al’umma a hannunsa ciki kuwa har da waɗanda a yanzu suke damawa da kuma waɗanda za su zo nan gaba. Wannan ya biyo bayan yadda Gwamnatin Jihar Zamfara ta sake fitar da jerin wasu takardun bayanai ne, waɗanda suke…
Read More
Gwamnan Oyo ya yi wa ma’aikata ƙarin Naira 25,000 a kan albashinsu

Gwamnan Oyo ya yi wa ma’aikata ƙarin Naira 25,000 a kan albashinsu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya bayyana cewa ma’aikatan jihar da ‘yan fansho za su riqa karɓar tallafin kuɗi na Naira 25,000 da kuma N15,000 duk wata na tsawon watanni shida har sai an cimma matsaya kan sabon mafi ƙarancin albashi. Ya kuma jaddada muhimmancin ma’aikata da al’ummar jihar wajen haɗa hannu da gwamnatin jihar domin bunƙasa tattalin arzikin jihar na tsawon lokaci. Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga ma’aikatan a ofishin gwamna, Sakatariya, Agodi a Ibadan. Ya yi nuni da cewa duk da cewa gwamnatinsa za ta…
Read More
Nijar ta nemi Togo ta shiga tsakani a rikicinsu da ECOWAS

Nijar ta nemi Togo ta shiga tsakani a rikicinsu da ECOWAS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin sojan Nijar ta nemi Shugaban Ƙasar Togo, Faure Gnassingbe ya shiga tsakani a tattaunawa da ƙasashen duniya musamman ma Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Afrika ta Yamma (ECOWAS) wadda ta ƙaƙaba wa Nijar takunkumi tun bayan juyin mulki. Ministan tsaron Nijar, Janar Salifou Mody ne ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da Shugaba Gnassingbe a Lome babban birnin ƙasar ranar Litinin. Ya kuma nemi Togo ta tsayawa Nijar a yarjejeniyar janye sojojin Faransa daga ƙasar ta yankin Sahel. "Yana da muhimmanci a koyaushe mu tunatar da abokan kawancenmu cewa, ƙofar Nijar a buɗe…
Read More
Majalisar Dattijan Nijeriya na son a tsagaita wuta a Gaza

Majalisar Dattijan Nijeriya na son a tsagaita wuta a Gaza

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattijan Nijerya ta buqaci gwamnatin tarayyar ƙasar ta haɗa kai da wasu ƙasashe domin yin kira a tsagaita buɗe wuta a rikicin Isra’ila da Hamas. Tun a ranar 7 ga watan Oktoba ne sojojin Isra'ila suke yin ruwan bama-bamai a Gaza, bayan mayaqan Hamas sun ƙaddamar da harin da ya yi sanadin mutuwar mutum 1,400 a Isra'ila, waɗanda mafi yawansu fararen hula ne, a cewar hukumomin Isra'ila. A cewar ma'aikatar lafiya ta Hamas, adadin waɗanda suka mutu a Gaza ya zarce mutum 10,000 ciki har da yara sama da 4,000. A wani ƙudiri…
Read More
’Yan bindiga sun yi wa masu taron mauludi yankan rago a Katsina

’Yan bindiga sun yi wa masu taron mauludi yankan rago a Katsina

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja ’Yan bindiga sun yi wa mutane yankan rago a wani taron Mauludi a yankin Kusa da ke Ƙaramar Hukumar Musawa a Jihar Katsina. ’Yan bindigar sun kashe mutumu 25, baya ga wasu 17 da suka tsallake rijiya da baya da aka kwantar a Babban Asibinin Musawa da kuma Asibitin Koyarwa na Katsina, a sakamkon raunukan da suka samu a harin. Manhaja ta gano mahalartar Mauludin sun zo taron ne daga ƙauyuka daban-daban na ƙanana hukumomin Musawa da kuma Matazu. Ɗaya daga cikinsu da aka kai Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina ya ce,…
Read More
Ranar Kimiyya Ta Duniya: UNESCO ta jaddada muhimmancin kimiyya ga cigaban duniya

Ranar Kimiyya Ta Duniya: UNESCO ta jaddada muhimmancin kimiyya ga cigaban duniya

Darakta Janar ta Hukumar Bunƙasa Ilimi da Al’adu ta Duniya (UNESCO), Ms. Audrey Azoulay, ta jaddada tasirin da kimiyya ke da shi wajen samar da ingantacciyar duniya. Ta bayyana haka ne a cikin wani sakon da ta gabatar na bikin ranar kimiyya ta duniya don haɓaka zaman lafiya da ci gaba a ranar 10 ga Nuwamba, 2023. A cewarta, kimiyya ta taimaka wajen rage yaɗuwar cututtuka kamar COVID-19, baƙon dauro, da foliyo ta hanyar samar da allurar rigakafi. Haka kuma, ta ce UNESCO na tunawa da ranar Kimiyya ta Duniya ce don inganta zaman lafiya da ci gaba a kowace…
Read More
Zaɓen Bayelsa, Imo, Kogi: Ban da nuna halin a-yi-rai-ko-a-mutu, kiran Kwamitin Abdulsalami ga ‘yan siyasa

Zaɓen Bayelsa, Imo, Kogi: Ban da nuna halin a-yi-rai-ko-a-mutu, kiran Kwamitin Abdulsalami ga ‘yan siyasa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kwamitin Wanzar da Zaman Lafiya na Ƙasa, Janar Abubakar Abdulsalami (rtd), ya yi kira ga jam'yyun siyasa da magoya bayansu da a guji nuna halin a-yi-rai-ko-a-mutu yayin zaɓen gwamnonin da za a gudanar ranar Asabar a jihohin Bayelsa da Kogi da kuma Imo. Abdulsalami ya yi wannan kira ne yayin da jam'iyyin siyasa su 18 da za su fafata a zaɓen gwamna a Jihar Kogi suka rattaɓa hannun kan yarjejeniyar zaman lafiya ranar Laraba a jihar. Da yake jawabi ta bakin wakilinsa Cardinal John Onaiyekan, tsohon shugaban ƙasar ya ce: “Wannan taro na da muhimmanci saboda…
Read More
Ƙungiyar Marubuta ta Ƙasa reshen Jihar Kano ta yi sabbin shugabanni

Ƙungiyar Marubuta ta Ƙasa reshen Jihar Kano ta yi sabbin shugabanni

Daga IBRAHIM HAMISU, Kano Ƙungiyar marubuta ta ƙasa reshen Jihar Kano, wato Association of Nigerian Authors (ANA) ta yi sabbin shugabanni da ya biyo bayan taron da ya gudana a ɗakin karatu na Murtala Muhammed ranar Lahadi da ta gabata. An dai yi zaɓen ƙungiyar ne yayin gabatar da manyan taruka da ta saba gudanarwa duk ƙarshen wata. An kuma zavi Dr.Murtala M. Uba wanda malami ne a sashen ilimin nazarin ƙasa wato (Geography) da ke jami'ar Bayero Kano a matsayin sabon shugaban ƙungiyar. Jim kaɗan bayan kammala zaɓen ne dai, sabon shugaban Dr. Murtala Uba ya ce, za su…
Read More
Kowa ya yi rubutu mai kyau zai samu karɓuwa – Ado Ahmad MON

Kowa ya yi rubutu mai kyau zai samu karɓuwa – Ado Ahmad MON

"Kyakkyawar mu'amala da mutane tasa ake karrama ni" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Sunan Ado Ahmad Gidan Dabino (MON) Sani Mai Nagge, ba ɓoyayye ba ne a duk faɗin ƙasar nan, ba ma tsakanin marubuta da masu shirya finafinai ba, har ma da manazarta na ƙasa da ƙasa. Ya yi rubuce-rubuce da dama cikin harsunan Hausa da Turanci, a ciki har da littafin da yanzu haka ya shiga cikin manhajar koyar da Hausa a manyan makarantun sakandire na qasar nan. Ya samu shaidar karramawa iri-iri da suka jawo masa ɗaukaka a duniya fiye da duk wani marubucin Hausa. A zantawarsa da…
Read More