Editor

9513 Posts
Gobarar tanka ta jikkata sama da mutum 20 a Kaduna

Gobarar tanka ta jikkata sama da mutum 20 a Kaduna

Daga BASHIR ISAH Aƙalla mutum 20, ciki har da jami'an kwana-kwana da 'yan banga suka jikkata sakamakon gobarar tankar mai da ta auku ranar Juma'a a Jihar Kaduna. MANHAJA ta kalato cewar, gobarar ta auku ne a daidai lokacin da ake sauke mai daga tankar a wani gidan mai da ke Rigasa cikin yankin Ƙaramar Hukumar Igabi a jihar. Da yake tabbatar da aukuwar iftila'in, Daraktan Hukumar Kwana-kwana na Jihar, Paul Aboi, ya ce gobarar ta ji wa wasu jami'ansu su biyar da wasu 'yan bangan jihar haɗi da wasu masu wucewa da dama raunuka. Jami'in ya ɗora alhakin faruwar…
Read More
Irin ta’asar da Yahudawa ke yi mana a Palastinu – Jakada Shawesh

Irin ta’asar da Yahudawa ke yi mana a Palastinu – Jakada Shawesh

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Jakadan Ƙasar Palastinu a Nijeriya, Abdullah Shawesh, ya bayyana irin ta’asar da ya ce Ƙasar Isra’ila (wato Yahudawa) suke yi wa al’ummar Palastinu na kisan gilla da kisan kiyashi kan waɗanda ba su ji ba ba su gani ba, kamar ƙananan yara da mata, inda kawo yanzu aka kashe kimanin Palastinawa fiye da mutum 6,000, waɗanda fiye sa rabinsu yara ne ƙanana. Shawesh ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai, ciki har da Blueprint Mahhaja, a ofishin jakadancin Palastinu da ke Abuja ranar Laraba. Idan za a iya tunawa, a ranar 7…
Read More
Waliyyan ango sun nemi a mayar musu da sadaki don su maida inda aka aro

Waliyyan ango sun nemi a mayar musu da sadaki don su maida inda aka aro

Daga AISHA ASAS  Idan ba ka mutu ba, aka ce komai kana gani. Wani sabon salo, wai Bature da feƙe. A ranar Larabar da ta gabata a Jihar Sakkwato a wata unguwa da ake kira Zoramawa aka yi taro na ji da gani da ƙudirin neman auren wata yarinya da saurayinta da suka jima su na yin soyayya.  Taron da ya ɗauki ilahirin dangin yarinyar lokaci wajen shiri na  kwalliya da kuma kayan abincin da aka shirya don tarbon dangin ango, waɗanda suka haɗa da lafiyayyun kaji da makusantan uwar amarya suka tabbatar kowacce ɗaya daga ciki an siye ta…
Read More
Shan fetur ya ragu zuwa lita miliyan  44.3 kowacce rana a Nijeriya

Shan fetur ya ragu zuwa lita miliyan  44.3 kowacce rana a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Amfani da man fetur na cikin gida na ƙasar Nijeriya ya ragu sosai daga litoci miliyan 66.7 da ake sha a kullum a faɗin ƙasar zuwa litoci miliyan 44.3 a kowacce rana.  Shugaban zartarwa na hukumar kula da man fetur ta NMDPRA, Farouk Ahmed Ahmed shi ya bayyana haka a jawabinsa na buxe taro a taron 'Oil Trading and Logistics' (OTL) na makon Afirka na bana, shekarar 2023, da aka gudanar ranar Litinin a jihar Legas. A cewarsa, an samu raguwar kaso 33.58 a kan yawan man da ake sha a kullum.  A jawabin nasa, shugaban…
Read More
Za mu ɓullo da sabon tsarin karɓar haraji – Gwamnatin Tarayya

Za mu ɓullo da sabon tsarin karɓar haraji – Gwamnatin Tarayya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Nijeriya na shirin rage yawan harajin da gwamnatin tarayya da na jihohi ke karɓa daga sama da 60 zuwa ƙasa da 10, shugaban kwamitin sake fasalin harajin ne ya bayyana hakan a ranar Talata. Za a ɓullo da sabon tsarin a wani ɓangare na sauye-sauyen da za a samu wajen gudanar da harkokin kasuwanci cikin sauƙi da kuma ƙara samun kuɗaɗen shiga. Nijeriya, ƙasar da ta fi kowacce ƙarfin tattalin arziki a nahiyar Afirka, tana da kaso 10.8 cikin 100 na haraji da GDP, wanda ɗaya ne daga cikin ƙasashe mafiya ƙarancin wannan adadin…
Read More
Cibiyar horas da kuratan sojoji ta DEPOT ta yaye mutum 6,315 a Zariya

Cibiyar horas da kuratan sojoji ta DEPOT ta yaye mutum 6,315 a Zariya

Daga ISAH GIDAN BAKKO a Zariya A ranar Asabar da ta gabata, cibiyar horas da kuratan sojoji da aka fi sani da' Depot Nigerian Army'' da ke Zariya ta ƙyanƙyashe kuratan sojoji har 6,315 karo na 85. A jawabinsa wajen bikin kammala horas da sojojin, babban kwamandan sojojin Nijeriya Laftana Janar Taoureed Lagbaja ya ja kunnuwan kuratan da aka yaye da su zama sojoji nagari a duk inda aka tura su aiki a ciki da wajen Nijeriya. Laftana Janar Lagbaja ya kuma ce rundunar sonojin Nijeriya da ya ke yin shugabanci za ta ƙara tashi tsaye na ganin ta qara…
Read More
Jega ya ƙalubalanci INEC kan ƙin loda sakamakon zaɓen Shugaban Ƙasa a manhajar IReV

Jega ya ƙalubalanci INEC kan ƙin loda sakamakon zaɓen Shugaban Ƙasa a manhajar IReV

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega ya ce tilas ne Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta binciki musabbabin rashin shigar da sakamakon zaɓen Shugaban Ƙasa zuwa manhajar duba sakamakon zaɓen INEC (IReV). A wata hira da ya yi da gidan talabijin na ARISE, tsohon Shugaban hukumar ta INEC ya ce zai iya danganta da yawa daga cikin ƙalubalen da aka fuskanta a lokacin babban zaɓen amma ya kamata a duba batun shigar da sakamakon zaɓe. “Kuma idan kun kasance kuna da ƙwarin gwiwa kan tsarin sai kuma a…
Read More
Yadda cire tallafi ke ƙara haifar da gagarumar matsalar fetur a Nijeriya

Yadda cire tallafi ke ƙara haifar da gagarumar matsalar fetur a Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Watanni biyar kenan bayan Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin fetur, yayin da ‘yan Nijeriya suka afka cikin matsananciyar tsadar rayuwa, yanzu kuma wasu gaggan matsalolin da ke sake dabaibaye hada-hadar shigo da tataccen fetur cikin Nijeriya daga daga waje, sai bijirowa suke yi su na kwankwatsar ‘yan Nijeriya, ta hanyar zaizaye masu ɗan abin da suke samu na yau da kullum. Bayan cire tallafin fetur da lamarin ya kai ga har lita 1 ta kai N617, Gwamnatin Tarayya ta ce za ta tsame kan ta daga shigo da fetur, domin bai wa ‘yan…
Read More
Shari’ar zaɓen 2023: Yadda Tinubu ya yi zarra a Kotun Ƙoli

Shari’ar zaɓen 2023: Yadda Tinubu ya yi zarra a Kotun Ƙoli

•Kotun ta yi fatali da shaidar takardun Chicago•Ta raraki Peter Obi•Tinubu ye nemi haɗin kai don gina Nijeriya•Atiku da Obi su jira zuwa 2031, cewar Ganduje•PDP da LP sun maida martani•Buhari ya yi maraba da hukuncin Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun Ƙolin Nijeriya ta tabbatar da nasarar Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasar na 2023. Hukuncin na alƙalai bakwai ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Inyang Okoro ya ce, “a ƙarshe, bayan warware duk wasu lamurra game da ɗaukaka ƙarar, zan iya cewa babu hujjoji masu ƙwari game da ɗaukaka ƙarar, saboda haka an yi watsi…
Read More
WHO da UNICEF za su yi wa ‘yan mata miliyan 7.7 rigakafin cutar kansar mahaifa a Nijeriya

WHO da UNICEF za su yi wa ‘yan mata miliyan 7.7 rigakafin cutar kansar mahaifa a Nijeriya

Nijeriya a hukumance ta shigar da allurar rigakafin cutar HPV a cikin tsarin rigakafinta na yau da kullum, da nufin kai wa yara mata miliyan 7.7 agaji cikin zagaye guda na allurar rigakafin cutar, wanda ya kasance mafi girman irinsa a yankin Afirka. Ministan Lafiya da Walwalar Jama'a, Muhammad Ali Pate, ya bayyana matukar damuwarsa kan cutar ta kansar mahaifa, yana mai cewa, "Asarar mata kusan 8,000 a duk shekara daga cutar da ake iya rigakafinta ba abu ne da za a amince da shi ba.“ Pate ya jaddada cewa ceton rayuka da tabbatar da ingantaccen kiwon lafiya su ne…
Read More