Editor

9513 Posts
Ma’aikatan NIPOST sun hana sabon shugaban da Tinubu ya naɗa musu shiga ofis

Ma’aikatan NIPOST sun hana sabon shugaban da Tinubu ya naɗa musu shiga ofis

Ma'aikatan Hukumar Tura Saƙonni (NIPOST) a babban ofishin hukumar da ke Abuja, sun yi zanga-zanga tare da rufe ma'aikatar saboda rashin amincewa da naɗa Tola Odeyemi a matsayin sabon shugaban hukumar da Shugaba Bola Tinubu ya yi. A makon da ya gabata Kakakin Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, ya bada sanarwar cewa Shugaba Tinubu ya yi sabbin naɗe-naɗe a hukumomin sadarwa ciki har da hukumar NIPOST. Sai dai jim kaɗan bayan sanar da naɗin Odeyemi, rahotanni suka nuna an sake maida babban jami'in hukumar da aka tsige da fari. An ga Adepoju a cikin wani faifan bidiyo da aka yaɗa yana…
Read More
Duwatsun Falasɗinawa da boma-boman Yahudawa

Duwatsun Falasɗinawa da boma-boman Yahudawa

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Zubar da jinin Falasɗinawa daga ƙarfin sojan Isra’ila ba wani sabon abu ba ne. Tun lokacin da Isra’ila ta samu galabar a yaqi da ƙasashen Larabawa a 1967 a ke ta samun mamaye yankunan Falasɗinawa ba ƙaƙƙautawa kuma ya zama tamkar a jefe ka kashin awaki ne kuma a hana ka kuka. Ai aƙalla kuka kan ragewa mutum baƙin ciki kuma takaici. Shekaru gommai da su ka wuce a kan ga ’yan yaran Falasɗinawa na ɗaukar duwatsu su na jifar sojojin Isra’ila da ke cikin tankokin yaƙi. Kowa ya san sakamakon mai dutse ya jefi…
Read More
Ana zargin almundahana a rabon kayan tallafin Kebbi 

Ana zargin almundahana a rabon kayan tallafin Kebbi 

*An dakatar da rabon tallafin Argungu Daga JAMIL GULMA a Kebbi  A ranar Juma'ar da ta gabata ne Gwamnan Jihar Kebbi, Malam Nasir Idris wanda shine Ƙauran Gwandu, ya ƙaddamar da rabon kayan tallafi a Ƙaramar Hukumar Maiyama, don rage raɗaɗin matsin tattalin arziki ga al'ummar jihar, inda kuma daga nan ya umarci kowacce ƙaramar hukumar mulki ta je ta raba a yankinta. Sai dai ba a nan gizo ke saƙa ba, saboda rabon kayan ya samu tarnaƙi yayin da a ke zargin tafka almundahana a waɗansu ƙananan hukumomi. Wata mata da ba ta so a bayyana sunanta ba ta…
Read More
Bahaushe mai tashi mu je

Bahaushe mai tashi mu je

Da farko ina amfani da wannan kalma ce domin mu faɗakar da juna ta fuskar gano illar ma su ɗabi'a ta tashi mu je. kalmar tashi mu je daga jin ta za a fahimci ta tattaro yaudara da ƙarya tare da ba ta lokaci ga wanda duk a kai ma hakan. Jama'a har kullum mu riƙa yi wa kawunan mu awo na adalci a madadin ga matsala a tattare da mu a gefe mu nai ma wasu kallon su ne ma su aikata laifuka. Misalin tashi mu je, mutum ne ka na zaman ka zai zo ko kuma ya kirawo…
Read More
Yadda sabbi da tsaffin gwamnoni suka halarci jana’izar Sardaunan Dutse

Yadda sabbi da tsaffin gwamnoni suka halarci jana’izar Sardaunan Dutse

Gwamnan Jihar Jigawa, Mal. Umar A. Namadi da takwaransa na Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, haɗa da tsohon Gwamnan Jigawa, Sule Lamido da tsohon Gwamnan Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso na daga cikin tarin jama'ar da suka halarci jana'izar marigayi Sardaunan Dutse, Sheikh Dr. Bello Maitama Yusuf. A ranar Juma'ar da ta gabata Allah Ya yi wa Bello Maitama rasuwa a gidansa da ke Tarauni, Kano, yana da shekara 76. A halin rayuwarsa, Bello Maitama ya taɓa riƙe muƙamin Ministan Cinikayya da wasannin motsa jiki a Jamhuriyya ta ɗaya ƙarƙashin Gwamnatin marigayi Ahaji Shehu Shagari. Haka nan, ya yi sanatan Jigawa…
Read More
Shan miyagun ƙwayoyi na neman kassara matasan Nijeriya

Shan miyagun ƙwayoyi na neman kassara matasan Nijeriya

A wannan makon, wasiƙata za ta fita ne kai tsaye ga matasa akan batun annobar ta’ammuli da miyagun ƙwayoyi a tsakanin rukunan al’ummar Nijeriya, domin wata babbar barazana ce da tarnaƙi a ci gaban zamantakewa, tsaro da tattalin arziki. Matsala ce mai wuyar magani wadda a kevance ɗaya ce daga cikin gagararrun matsalolin da suka gunduri kowa, waɗanda suka tsunduma sabbin jinin shiga mawuyacin hali da yawaitar ayyukan ashsha. Masana sun tabbatar da cewa al’adar amfani da miyagun ƙwayoyin ba a kan daidai ba, ya na da alaƙar ƙut-da-ƙut wajen yaɗuwar miyagun laifuka a ƙasar nan. Bil hasali, yanayin da…
Read More
Ɗaukar matakin gaggawa shi ne mafita kan duk wata matsala

Ɗaukar matakin gaggawa shi ne mafita kan duk wata matsala

Tun daga lokacin da aka ayyana janye tallafin fetur mutane suka shiga mawuyacin hali, saboda ba wani matakin gaggawa da aka ɗauka don nunawa gwamnati matsalar da za a shiga. Ɗaukar matakin gyara da wuri ya fi komai. Na fahimci hakane a lokacin wani rikicin aƙida da wata mata ta taɓa haddasawa a Bauchi. Kwamishinan ’yan sanda na lokacin ya kira ’yan jarida ya faɗa mana mace ta haddasa rigimar amma bai san inda ta ke ba. Daga lokacin na fara bincike zuwa matuary a asibitin TH, saboda can aka kai gawarwaki kusan 40 da aka kashe lokacin rikicin aka…
Read More
Barace-baracen ƙananan yara a tituna abin dubawa ne

Barace-baracen ƙananan yara a tituna abin dubawa ne

Ga duk mai dubi zuwa ga yadda aka jefa Ƙananan Yara cikin harkar barace- barace, musamman a biranen ƙasar nan zai ga cewa akwai sosar zuciya mutaƙa, musamman ganin yadda yaran ke fama da wahala, sannan ga ɓata sunan Hausawa da abin ke jawowa. Akwai abubuwa da dama, waɗanda idan mutum ya yi dubi zuwa gare su za su dagula masa rayuwa ya ma rasa abin da ke masa daɗi, musamman idan aka duba yadda wasu abubuwa ke jawo wa rayuwar al’ummar da abin ya shafa. Wasu daga cikin waɗannan abubuwa, waɗanda kuma za mu iya cewa babu wani mai…
Read More
An yi jana’izar mahaifiyar tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Hajiya Halima

An yi jana’izar mahaifiyar tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Hajiya Halima

An yi jana'izar mahaifiyar tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan; Hajiya Halima (Dada) wadda Allah Ya yi wa rasuwa garin Gashuwa, shalkwatar ƙaramar hukumar Bade a jihar Yobe. Taron jana'izar ya samu halartar dandazon jama'a daga sassa daban-daban daga ciki da wajen Jihar Borno. Mahaltar sun haɗa da Gwamnan Jihar Yobe, Farfesa Babagana Umara Zulum da Mataimakinsa, Idi Barde Gubana da sarakuna da sauransu. Sanata Lawan ta bakin kakakinsa, Ezrel Tabiowo, ya yi godiya ga ɗimbin jama'ar da suka halarci taron jana'izar.
Read More
Gwamnan Kano ya rattaba hannu kan ƙwarya-ƙwaryar kasafin kuɗin 2023

Gwamnan Kano ya rattaba hannu kan ƙwarya-ƙwaryar kasafin kuɗin 2023

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnan Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu a ƙwarya-ƙwaryar kasafin kuɗin shekarar 2023 wanda ya kai Naira biliyan hamsin da takwas, da miliyan ɗari da casa’in da daya, da dubu dari biyar da talatin da biyar, da naira goma sha takwas da kobo goma sha biyu (N58, 191, 535, 018.12), inda ya zama doka. Yayin da yake sanya hannu a kasafin kuɗin, Engr. Abba Kabir Yusuf ya tabbatar wa al’ummar jihar Kano cewa gwamnatinsa za ta bi ƙa’idojin amfani da kasafin kuɗi domin kuɗaɗen da aka ware za a yi amfani da su…
Read More