Editor

9513 Posts
Allah ya yi wa mahaifiyar tsohon shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya rasuwa a Yobe

Allah ya yi wa mahaifiyar tsohon shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya rasuwa a Yobe

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN, Damaturu Allah ya yi wa mahaifiyar tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmed Ibrahim Lawan; Hajiya Halima (Dada) rasuwa a mahaifarsa dake garin Gashuwa, shalkwatar ƙaramar hukumar Bade a jihar Yobe. Yayin da yake sanar da rasuwar, Malam Yahaya Mato, a madadin iyalai da 'yan uwa, ya bayyana cewa Allah ya yi wa Hajiya Dada; 'yar kimanin shekaru 90 a duniya rasuwa a Unguwar Katuzu dake cikin garin Gashuwa. Haka zalika, sanarwar ta bayyana cewa za a yi jana'izar marigayiyar ne gobe Lahadi, 15 ga watan Oktoban 2023, da misalin ƙarfe 11:00 na rana a masallacin ƙofar…
Read More
An karrama ɗan shekaru 70 wanda bai taɓa zuwa makaranta ba da digirin girmamawa

An karrama ɗan shekaru 70 wanda bai taɓa zuwa makaranta ba da digirin girmamawa

Daga WAKILINMU Wani ɗan Nijeriya mai shekaru 70 da haihuwa, Injiniya Hadi Usman, ya samu lambar yabo ta digirin digirgir a fannin kimiyya daga jami’ar jihar Gombe bayan ya ƙirqƙiro injin janareta maras amfani da fetur. A cewar babban mataimaki na musamman kan harkokin yaɗa labarai ga gwamnan jihar Gombe, Safianu Danladi Mairiga akan manhajar X, an bai wa Usman wannan digiri ne a taron da aka kammala na 10, 11, 12, da 13 na jami'ar jihar Gombe. Hadi wanda aka ce bai taɓa zuwa makarantar boko ba, ya kafa gidan rediyo, da na’urar watsa labarai ta rediyo. Sannan ya…
Read More
An sallami ɗan sanda bisa zargin fyaɗe a Binuwai

An sallami ɗan sanda bisa zargin fyaɗe a Binuwai

Daga WAKILINMU Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya a Jihar Benuwai ta sallami wani ɗan sanda mai suna Belasa Iyangedue bisa zargin sa da yi wa wata yarinya ’yar shekara 16 fyaɗe a lokacin da ta ke tsare a ofishin 'yan sanda. An rawaito cewa kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Batholomew Onyeka ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke Makurdi. Onyeka ya ce rundunar ’yan sandan Nijeriya a matsayinta ta hukuma mai ƙoƙarin tabbatar da ɗa’a ba za ta amince da irin wannan laifin da ya saba wa ƙa’idojin aikin ba. Ya bayyana…
Read More
Tinubu ya yi sabbin naɗe-naɗe a fannin sadarwa

Tinubu ya yi sabbin naɗe-naɗe a fannin sadarwa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi sabbin naɗe-naɗen muƙamai biyar a wasu hukumomin da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Sadarwa, Ƙirƙire-Ƙirƙire da Tattalin Arziki na Zamani ta Tarayya, a ranar Laraba. Waɗanda aka naɗe su ne Aminu Maida, wanda ya taɓa zama Babban Darakta na Fasaha da ayyuka a Nijeriya 'Inter-Bank Settlement System Plc' (NIBSS), wanda yanzu ya naɗa Mataimakin Shugaban Hukumar (EVC) a matsayin Shugaba na Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC). An sake naɗa Shugaban Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA) Kashifu Inuwa Abdullahi a karo na biyu. A cewar wata sanarwa da mai ba shi…
Read More
Mutum 20 sun mutu sakamakon ɓarkewar cutar Mashaƙo a Kaduna

Mutum 20 sun mutu sakamakon ɓarkewar cutar Mashaƙo a Kaduna

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Aƙalla mutane 20 ne aka tabbatar sun mutu sakamakon ɓarkewar cutar Mashaƙo a Jihar Kaduna. Babban babban Jami’in hukumar kula da lafiya a matakin farko na ƙasa, Dakta Faisal Shuaibu ne ya bayyana hakan a ranar Laraba, inda ya ce an samu mutum 156 waɗanda suka kamu da cutar a jihar. Da yake zantawa da manema labarai a cibiyar kula da cutar mashaƙo ta jihar Kaduna da ke asibitin koyarwa na Barau Dikko a babban birnin jihar, Shu’aibu ya buq'ƙaci jama’a da su bi ƙa’idojin kiyayewa da aka gindaya, su kuma lura da alamun cutar domin…
Read More

’Yan bindiga sun yi awon gaba da malami a motar gawa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wasu ’yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba sun yi garkuwa da wani malamin addinin Islama, Alfa Fasasi Ola Mejabi da ƙaninsa a Jihar Kogi. Malamin da sauran su su na miƙa ɗauke da gawar babban Limamin Ayegunle Gbede, Sheikh Musa Olorunkemi, daga Lokoja zuwa Ayegunle Gbede da ke ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi domin yi masa jana’iza a ranar Lahadin da ta gabata, inda suka yi karo da masu garkuwa da mutane. Ɗaya daga cikin mutanen da ke cikin motar da suka tsallake rijiya da baya ya shaida wa manema…
Read More
Eden Hazard ya yi ritaya daga buga ƙwallon ƙafa

Eden Hazard ya yi ritaya daga buga ƙwallon ƙafa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon ɗan ƙwallon ƙafar Chelsea, Eden Hazard ya sanar da yin ritaya daga qwallon lafa, bayan ya bar Real Madrid a ƙarshen kakar wasan da ta wuce. Hazard mai shekara 32, ya koma Real ne daga Chelsea a shekara ta 2019 a kan fam miliyan 89, amma wasa 54 na lig kawai ya bugawa aungiyar. Ya lashe kofin gasar firimiya biyu a Stamford Bridge. "Dole ne ka saurari kanka, kuma ka daina buga ƙwallo a lokacin da ya dace," inji Hazard wanda tun a watan Yuni ba shi da kulob. "Bayan shafe shekara 16 tare da…
Read More
Tinubu ya cire FCT daga tsarin Asusun Bai-ɗaya, ya ƙarfafa Wike kan tara kuɗin shiga

Tinubu ya cire FCT daga tsarin Asusun Bai-ɗaya, ya ƙarfafa Wike kan tara kuɗin shiga

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya cire Hukumar Birnin Tarayya FCTA daga tsarin Asusun Bai-ɗaya (TSA). Shugaban ya ce ɗaukar wannan mataki zai ƙarfafa wa Ministan Abuja, Nyesom Wike wajen sarrafa kuɗin shigar da Abuja ke tarawa yadda ya kamata wajen bunƙasa birnin. Da yake yi wa manema labarai jawabi a ranar Juma'a, Wike ya ce Tinubu ya amince da ƙirƙiro Hukumar Kula da Ma'aikata ta Abuja. Ya ce yin haka zai bada damar cigaban ma'aikatan FCT. Kafin wannan lokaci ma'aikatan yankin Abuja na kokawa kan rashin wannan hukuma wadda za ta kula musu da cigabansu a bakin aiki.
Read More
Ya binne ƙaninsa da ransa kan satar Naira 1,000 a Kogi

Ya binne ƙaninsa da ransa kan satar Naira 1,000 a Kogi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Larabar da ta gabata ne al’ummar Apamisede da ke Ƙaramar Hukumar Adavi ta Jihar Kogi suka shiga ruɗani yayin da aka binne wani yaro ɗan shekara takwas da ransa sakamakon satar kuɗi naira dubu ɗaya kacal (N1000) mallakin mahaifiyarsa. A cewar shaidar gani da ido, mahaifiyar yaron ta umurci babban ɗanta mai shekaru 19 da ya hukunta yaron saboda satar kudin. Babban yaya wajen aiwatar da umarnin mahaifiyarsa, ya yanke shawarar binne yaron da ransa har sai da makwabta nagari suka kawo masa ɗauki suka tono yaron da ke numfashi da ƙyar. Jami’in hulɗa…
Read More

Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 50, sun kama 114 a mako guda – Hedkwatar Tsaro

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hedikwatar tsaro ta ce sojojin Nijeriya sun kashe 'yan ta'adda 50 tare da kame wasu 114 cikin mako guda a hare-hare daban-daban a yankin Arewa maso Gabas da Arewa ta Tsakiya da kuma Arewa maso Yamma. Darakta mai kula da ayyukan yaɗa labarai na tsaro, Manjo Janar Edward Buba, ya bayyana haka ne yayin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar, ranar Alhamis a Abuja. Mista Buba ya ce sojojin sun kuma ceto mutane 49 da aka yi garkuwa da su a cikin mako guda. Ya ce dakarun Operation Haɗin Kai da…
Read More