Editor

9513 Posts
Gobe za a ƙaddamar da littafin ‘100+ questions before Nikkah’

Gobe za a ƙaddamar da littafin ‘100+ questions before Nikkah’

Daga AISHA ASAS Shahararriya kuma ƙwararriyar mai bayar da shawarwari kan zamantakewar aure da kuma rayuwa bakiɗaya, Khadija Ibrahim, marubuciya da ta jima tana gyara al'umma da alƙalaminta, ta shirya tsaf don bayar da ƙarin gudunmawa ga masu shirin yin aure, wato littafin da zai amsa tambayoyi ɗari har da ɗori da mata da maza suke buƙatar sani kafin su shige daga ciki. Littafin mai suna tambayoyi ɗari da ɗori kafin aure, wanda zai kasance a turance, wato '100+ questions before Nikkah' zai amsa kusan dukkan tambayoyin da ake buƙatar sani game da aure, waɗanda za su fitar da samari…
Read More

Tsohon Ministan Cikin Gida, Sanata Bello Maitama ya kwanta dama

Tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida, Bello Maitama Yusuf, ya riga mu gidan gaskiya yana da shekara 76. Wani na kusa da marigayin, Hussaini Dalhatu, shi ne ya tabbatar da rasuwar nasa a ranar Juma'a. Ya ce za a yi jana'izar Sardauna Dutse a fadar Sarkin Kano bayan an sauko daga Juma'a. A halin rayuwarsa, marigayin ya yi sanata daga shekarar 1999 zuwa 2007. Kuma ya riƙe muƙamin Ministan Harkokin Cikin Gida a 1981, sannan Ministan Kasuwanci 1982. An haifi Bello Maitama Yusuf ne garin Gwaram, Jihar Jigawa a shekarar 1947.
Read More
Gwamnan Zamfara ya yi kira ga malamai kan riƙo da gaskiya

Gwamnan Zamfara ya yi kira ga malamai kan riƙo da gaskiya

*Ya jaddada aniyarsa kan ƙaurace wa sulhu da 'yan bindiga A yau Juma’a, Gwamnan Dauda Lawal, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ƙauracewa duk wani batun sulhu da ɓarayi a faɗin Jihar Zamfara. Gwamnan Ya bayyana haka ne a yayin da ya halarci taron wa’azi na mako-mako da aka saba gudanarwa a Gusau, inda ya hori Malaman Addini da su kasance masu riƙo da gaskiya. Wata takardar sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta ce wannan taron wa’azin mako an kwashe shekaru ana gudanar da shi, kuma wannan shi ne karo na 1,…
Read More
Ana nuna damuwa kan yadda Tinubu ba ya kiran Zaman Majalisar Zartarwa

Ana nuna damuwa kan yadda Tinubu ba ya kiran Zaman Majalisar Zartarwa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bai kira taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya ba kwanaki 44 da kammala zaman majalisar da aka gudanar a ranar 28 ga watan Agusta. Hakan ya cigaba da haifar da ayar tambaya kan ko hakan na iya shafar harkokin mulki ko a'a? Majalisar Zartaswa ta Tarayya, wadda shugaban ƙasa ke jagoranta, ita ce Majalisar Zartarwa ta Gwamnatin Tarayyar Nijeriya kuma wani ɓangare na zartarwa. Matsayin tsarin mulki na FEC, kamar yadda yake ƙunshe a cikin Dokar Ayyuka na Ministoci, ita ce ta zama ƙungiya mai ba da shawara ga shugaban ƙasa. A…
Read More
EFCC ta ƙwato sama da Naira Biliyan 27 a hannun tsofaffin gwamnoni da ministoci

EFCC ta ƙwato sama da Naira Biliyan 27 a hannun tsofaffin gwamnoni da ministoci

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati (EFCC) ta Nijeriya ta bayyana cewa, ta ƙwato jimillar Naira 27,184,357,524.52 da dala 19,084,419.33 a wasu shari’o’i uku na karkatar da kuɗaɗe. Daga cikin wannan adadin da aka ƙwato, an gano Naira biliyan 12.7 ne daga hannun mutum ɗaya. Hukumar ta EFCC na binciken tsaffin gwamnoni da tsofaffin Ministoci da wasu jami’an gwamnati a faɗin ƙasar nan a ƙoƙarin da ta ke yi na yaƙi da cin hanci da rashawa. Muƙaddashin shugaban hukumar ta EFCC Abdukarim Chukkol ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai…
Read More
Hukumar Alhazai ta bai wa maniyyata wa’adin makonni uku su fara adashin gata

Hukumar Alhazai ta bai wa maniyyata wa’adin makonni uku su fara adashin gata

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta ce, hukumar na da tsawon makonni uku domin tattaunawa da masu yi wa alhazai hidima a ƙasar Saudiyya, inda ta buƙaci maniyyatan Nijeriya da su fara ajiye Naira miliyan 4.5 kafin lokacin aikin hajjin a matsayin adashin gata. Mataimakiyar Daraktar Hulɗa da Jama’a ta NAHCON, Fatima Sanda Usara a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, ta ce Masarautar ta sanya ranar 4 ga watan Nuwamba, 2023 don kammala taron share fage da masu ba da hidima, inda ta ce, kafin nan ya kamata hukumar ta yi kiyasin aniyar maniyyata aikin…
Read More
Sojoji sun yi wa ’yan bindiga mummunan ta’adi a Zamfara

Sojoji sun yi wa ’yan bindiga mummunan ta’adi a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce, kashe ’yan bindiga fiye da 100 a Ƙaramar Hukumar Maru ta Jihar Zamfara. Wannan na zuwa ne sa'o'i 24 bayan Babban Hafsan Tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa ya umarci dakarun su bi ’yan bindigar har mavoyar su don kawar da su. Rahotanni sun ce sashin sojin sama na rundunar Operation Hadarin Daji ce ta yi wannan aiki, bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa yan bindigar suna kan hanyar su ta kai hari a wani ƙauye. Majiya daga rundunar sojin ta ce, dakarun rundunar sun yi amfani da jirgin sama…
Read More
Haɗin mutum biyu-biyu 10 da suka fi zura ƙwallaye da ‘Assist’ a tarihin Firimiya

Haɗin mutum biyu-biyu 10 da suka fi zura ƙwallaye da ‘Assist’ a tarihin Firimiya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kamar yadda kowa ya sani ne cewa cin ƙwallo a gasar ƙwallon ƙafa yana buƙatar taimakawa ma'ana ‘Assist’, inda akwai wasu manyan ’yan wasan biyu-biyu da suka shahara wajen zuwa ƙwallaye da assist a gasar ƙungiyoyin Firimiya. Sanin kowa ne 'yan wasan Tottenham Harry Kane da Son Heung-min ne ke kan gaba, amma bayan da Bayern Munich da wasu daga cikin cikin ƙungiyoyi da dama ke neman ɗauko ɗan wasan na Ingila a wannan bazarar, shin za a kawo ƙarshen haɗakar? An yi ƙididdigar ƙungiyoyi 10 da suka fi samun yawan ƙwallaye da taimakawa a gasar…
Read More
Tinubu ya nemi Kotun Koli ta watsar da ƙarar Atiku bisa rashin bin ƙa’ida

Tinubu ya nemi Kotun Koli ta watsar da ƙarar Atiku bisa rashin bin ƙa’ida

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya buƙaci Kotun Kolin Nijeriya da ta yi watsi da ƙarar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya shigar, na ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu. Lauyoyin Tinubu ƙarƙashin jagorancin Wole Olanipekun (SAN) ne suka bayyana hakan, wanda a martanin da Atiku ya ɗaukaka, ya buƙaci Kotun Kolin ta yi watsi da ɗaukaka ƙarar da ya shigar na cin zarafi. A cikin ƙarar da Atiku ya shigar, ya buƙaci Kotun Kolin ta soke hukuncin da kotun sauraren ƙararrakin zaɓen shugaban…
Read More
Ku ceci rai kafin tambayar rahoton ’yan sanda – Minista ga asibitoci

Ku ceci rai kafin tambayar rahoton ’yan sanda – Minista ga asibitoci

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan lafiya da walwalar jama’a, Muhammad Ali Pate, ya buƙaci asibitocin ƙasar da su fifita ceton rayuka fiye da kowane abu. An dai yi ta cece-ku-ce a tsawon shekaru ga asibitocin da ke neman ‘yan sanda su kai rahoton harbin bindiga da waɗanda hatsari ya rutsa da su kafin a fara jinya, lamarin da ya kai ga rasa rayukansu a lokuta da dama. Amma da yake magana a gidan Talabijin na Channels a wani shiri 'Sunrise Daily' a ranar Laraba wanda Blueprint Manhaja ke sa ido a kai, Pate ya koka da wannan lamarin…
Read More