Editor

9513 Posts
Gwamna Lawal ya bada tabbacin tallafa wa makarantun sojoji a Zamfara

Gwamna Lawal ya bada tabbacin tallafa wa makarantun sojoji a Zamfara

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada aniyarsa ta tallafa wa makarantun sojoji da ke faɗun jihar. Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a lokacin da ya karɓi baƙuncin Shugaban makarantar sojoji ta Nigerian Army Education Corps (NAEC), Manjo Janar Bello Alhaji Tsoho, a Gusau, babban birnin jihar. Sanarwar da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta ce Shugaban makarantar ya kai ziyarar ne domin ƙarfafa alaƙa tsakanin makarantar da Gwamnatin Zamfara. Idris ya ƙara da cewa, Kwamandan ya nemi goyon bayan gwamnatin jihar kan ci gaba da kafa makarantun sosjoji a jihar. A cewarsa, “Gwamna Lawal…
Read More
A da ne mata suka fuskanci ƙalubalai a aikin jarida – Khadija Salihu

A da ne mata suka fuskanci ƙalubalai a aikin jarida – Khadija Salihu

"Girki na taka muhimmiyar rawa a zamantakewar aure" Daga AISHA ASAS Masu karatunmu Allah Ya kawo mu, sati ya zagayo, sannunku da ƙoƙarin bibiyar jaridar Manhaja. Shafin Gimbiya mai kawo maku fira da mata daban-daban kan sha'anin rayuwarsu, tun daga sana'o'insu ko ayyukan da suke yi, zuwa ƙalubalai da kuma nasarorin da suka samu. Shafi ne da ke ƙoƙarin ganin ya zama allon kallo ga mata, ta hanyar zaburar da su kan neman na kansu, taɓo ɓangarorin da za su share hawayen wasu mata su fahimci ba su kaɗai ne ke fuskantar matsalolin da suke ciki ba, kuma ilimi gare…
Read More
Ministan Labarai ya buƙaci NBC ta gyara ɗamararta

Ministan Labarai ya buƙaci NBC ta gyara ɗamararta

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya yi kira ga Hukumar Kula da Gidajen Talabijin da Rediyo ta Ƙasa, NBC, da ta sako masu ruwa da tsaki cikin harkokinta domin binciko kafafen da ke saɓa dokar yaɗa labarai. Idris ya yi wannan kira ne yayin ziyarar aikin da ya kai babban ofishin hukumar da ke Abuja. Ya ce akwai buƙatar NBC ta gyara salon aikinta maimakon ƙaƙaba takunkumi da tarar da takan yanka wa kafafen da ta samu da take doka. Ya ce, “Ban yarda cewa ƙaƙaba takunkumi shi ne kaɗai abin da NBC ta sani ba.…
Read More
Rikicin Sudan: Gwamna Lawal ya samar da agajin gaggawa ga ɗaliban Zamfara 66 da aka dawo da su

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal ya samar da agajin gaggawa ga ɗaliban Zamfara 66 da aka dawo da su

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samar da hanyar jin ƙai ga ɗalibai 66 ‘yan asalin Jihar Zamfara da aka dawo da su gida daga Sudan. Gwamnatin Jihar Zamfara ce ta tura Ɗalibai 66 karatu Sudan, waɗanda kuma ba su kammala karatunsu ba aka dawo da su sakamakon yaƙin da ya kaure. A wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa Kwamishinan Ilimi ne ya yi ƙarin haske ga Majalisar Zartaswar Jihar Zamfara a zamanta na ranar Litinin ɗin da ta gabata. Ya ƙara da cewa, ɗalibai 14 cikin 66…
Read More
Gudunmawar malamai ga harkar ilimi da cigaban ƙasa

Gudunmawar malamai ga harkar ilimi da cigaban ƙasa

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU A duk shekara, Majalisar Ɗinkin Duniya tana ware ranar 5 ga watan Oktoba, domin ta zama ranar da duniya za ta tuna da gudunmawar da malamai ke bayarwa wajen yaƙi da jahilci, koyar da ilimi ga yara masu tasowa da kuma horar da matasa da sauran masu nazari da bincike kan fannonin rayuwa daban-daban, domin su samu ƙarin ilimi da gogewa. Tun daga shekarar 1994 da aka fara tsayar da wannan rana duniya ke bukin ranar, wajen tattaunawa da nazarin yadda gwagwarmayar malamai da sadaukarwar su take samar da ilimi mai inganci, da ɗora al'umma…
Read More
Kotu ta ɗaure sojan Nijeriya shekara bakwai kan sace kuɗaɗen gwamnati

Kotu ta ɗaure sojan Nijeriya shekara bakwai kan sace kuɗaɗen gwamnati

Kotun soja ta ɗaure Daraktan kamfanin kula da kadarorin Sojojin Nijeriya, Manjo Janar Umaru Mohammed, shekar bakwai a gidan yari bayan da ta kama shi da laifin sace kuɗaɗen gwamnati. Kazalika, kotun ta kuma umarci mai laifin da ya maido da kuɗaɗe Dalar Amurka 2,178,900 da Naira biliyan 1.65 da ya sata. Kotun wadda ke zamanta a Abuja, ta yanke hukuncin ne a ranar Talatar da ta gabata. An kama Mohammed da laifuka 14 daga cikin laifuka 18 da ake zarginsa da aikatawa, da suka haɗa da karkatar da kuɗaɗen gwamnati, amfani da bayanan ƙarya, haɗin baki da dai sauransu.…
Read More
A cikin kowane mutum takwas guda na fama da taɓin hankali – MƊD

A cikin kowane mutum takwas guda na fama da taɓin hankali – MƊD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa, halin da duniya ke ciki a yau a cikin kowane mutum takwas za a tarar da guda na fama da taɓin hankali. Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres ne ya nayyana haka cikin sanarwar da ya fitar a ranar Talata albarkacin Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa ta Duniya ta bana. Sakataren ya bayyana lafiyar ƙwaƙwalwa a matsayin mai muhimmanci wanda da ita rayuwa kan inganta, haka ma da ita al'umma take bunƙasa.Ya ƙara da cewa, mata da matsa na daga cikin waɗanda ake samu suna fama da matsalar taɓin hankali. Ya ce, masu fama da…
Read More
Ambaliya ta kashe mutum 45 a jihohi 13 – NEMA

Ambaliya ta kashe mutum 45 a jihohi 13 – NEMA

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta ce ambaliyar ruwa ta kashe mutum 45 sannan ta raba wasu 171,545 da muhallansu a jihohi 13. Ta ƙara da cewa, an fuskancin ambaliyar ne sakamakon ruwan sama mai ƙarfin da ake samu a wannan damina. Wani jami'in hukumar mai suna Dapo Akingbade, shi ne ya bayyana hakan a wajen wani taro da aka shirya a Abuja kwanan nan. A cewar Akingbade, ya zuwa 7 ga watan Oktoba bayanai sun nuna an samu ambaliyar ruwa a jihohi 13, tare da lalata sashen gidaje 22,666, kana gidaje 5,358 sun lalace baki ɗaya. Ya…
Read More
An damƙe mutum biyu bisa zargin kashe ɗan jarida, Hamisu Danjibga a Zamfara

An damƙe mutum biyu bisa zargin kashe ɗan jarida, Hamisu Danjibga a Zamfara

'Yan sanda a Jihar Zamfara sun damƙe wasu mutum biyu da ake zargi da kashe ɗan jarida Hamisu Danjibga a jihar. Kwamishinan 'Yan Sandan Jihar, Mohammed Dalijan, ya ce ana zargin wani ɗan ɗan'uwan marigayin, Mansur Haruna tare da abokinsa Ibrahim Nababa su ne suka kashe ɗan jaridar. Kwamishinan ya bayyana haka ne a ranar Talata a lokacin da aka baje waɗanda ake zargin a Hedikwatar 'Yan Sanda da ke Gusau, babban birnin jihar. Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne bayan da jami'ansu suka sunkuya bincike biyo bayan kashe marigayin. A cewar Kwamishinan, "Babban wanda ake zargi shi…
Read More
Arewa ina mafita? Ya kamata mu farka daga barci ‘yan Arewa!

Arewa ina mafita? Ya kamata mu farka daga barci ‘yan Arewa!

Daga ABDULLAHI JIBRIL LARABI Hasbinallahu Wa Ni'imal Wakil! 'Yan bindiga sun kwashi mata a Federal University Dutsen-Ma. Mako biyu da suka wuce sun kwashi mata a Federal University Gusau. Wannan wace irin masifa ce take neman mamaye Arewa? Shin haka za mu zauna mu zuba ido don abin ba akanmu yake faruwa ba ko a kan Makusantanmu? Ina manyan malamanmu na addini? Ba za a ji muryoyinsu ba sai akan saɓanin aƙida ko siyasa? Shin ina manyan yan siyasar Arewa? Sai lokacin Kamfe za su san da zamanmu kenan?Ina manyan sarakunanmu na Arewa? Sai lokacin bukukuwan Sallah za a ji…
Read More