Editor

9513 Posts
Shehun shehunan Larabci a Nijeriya, Ogunbiyi

Shehun shehunan Larabci a Nijeriya, Ogunbiyi

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Na taɓa wani rubutu da daɗewa ina mai cewa duk Musulmin Nijeriya na jin harshen Larabci ko da kuwa basa iya magana kai tsaye da harshen. In mun duba yadda a kan ba da umurni da harshen ka ga sun yi abun da a ka faɗa za a iya amincewa cewa batun haka ya ke. Alaƙa da addini kasancewar da harshen a ke magana ya yi matuƙar taimakawa wajen fahimtar harshen. A sallar Juma’a liman zai ce “ƙuumuu ila salaatikum…” sai ka ga manya da yara duk sun miƙe don fahimtar abun da a ka…
Read More
Kotun Ƙoli ta sanar da ranar da za ta yanke hukuncin shari’ar belin Kanu

Kotun Ƙoli ta sanar da ranar da za ta yanke hukuncin shari’ar belin Kanu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A jiya Alhamis ne Kotun Ƙolin Nijeriya ta tsayar da ranar 15 ga watan Disamba domin yanke hukunci kan ƙarar da Gwamnatin Tarayya ta shigar a kan hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara da ta soke tuhumar da ake wa shugaban ƙungiyar masu fafutukar kafa ƙasar Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, tare da bayar da umarnin a sake shi. A zaman sauraron ƙarar na jiya Alhamis, wasu mutane biyar na Kotun Ƙoli ƙarƙashin jagorancin Kudirat Kekere-Ekun sun dage sauraron ƙarar don yanke hukunci bayan ta ɗauki taƙaitaccen bayani daga lauyoyi daga ɓangarorin. A yayin da take ci…
Read More
Ambaliyar ruwa ta raba mutane 563 da muhallansu a Adamawa

Ambaliyar ruwa ta raba mutane 563 da muhallansu a Adamawa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ambaliyar ruwan sama ta raba mutane 563 da ke Unguwan Tana a Ƙaramar Hukumar Yola ta Gabas a jihar Adamawa. Mutanen da iftila’in ya shafa, a yanzu haka sun samu mafaka a makarantar sakandare ta je ka ka dawo ta GDS da ke yankin Limawa-Jimeta, a Yola babban birnin jihar. Shugaban makarantar Musa Hassan Jada ya bayyana cewa, mutanen da abin ya shafa sun tare a ajujuwa bakwai na makarantar. Kazalika, mataimakin gwamnan jihar Kaletapwa George Farauta, ya ziyarci Unguwan Tana domin duba irin varnar da ambaliyar ruwan ta janyo. Bugu da ƙari, George…
Read More
Kotu ta tabbatar da zaɓen Gwamna Idris na Kebbi

Kotu ta tabbatar da zaɓen Gwamna Idris na Kebbi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe ta Jihar Kebbi, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Ofemai Ofem, ta yi watsi da ƙarar da jam’iyyar adawa ta PDP ta shigar tana ƙalubalantar nasarar Gwamna Nasir Idris. Da yake yanke hukuncin a gaban lauyoyi da jiga-jigan jam’iyyar APC, tun da farko alƙalin ya yi fatali da zarge-zargen da ake yi wa mataimakin gwamnan jihar Umar Tafida, bayan da ya miƙa takardar shaidar makarantar da ya halarta a matsayin shaida. A game da kura-kuran zaɓe, kotun ta ce kimanin shaidu 17 daga hukumar zaɓe ta INEC sun tabbatar da cewa zaɓen ba shi…
Read More
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Dattawa ta gayyaci Ribadu da shugabannin tsaro

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Dattawa ta gayyaci Ribadu da shugabannin tsaro

*Kotun soji ta samu Janar Muhammed da laifin karkatar da miliyoyin Dala Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Dattawan Nijeriya ta ƙuduri aniyar yi wa hafsoshin tsaron ƙasar kiranye, saboda taɓarɓarewar tsaro a ƙasar, musamman Arewacin Nijeriya. Majalisar Dattijai ta ɗauki matakin ne a jiya Alhamis bayan tattaunawa kan batutuwan yin garkuwa da wasu ɗalibai mata guda biyar na Jami’ar Tarayya Dutsin-Ma dake Jihar Katsina a ranar Laraba bayan da Sanata Yar’Adua mai wakiltar yankin Katsina ta Tsakiya a majalisar ya gabatar da ƙudirin. Waɗanda za a gayyace sun haɗa da; Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Musa; Babban Hafsan Sojin…
Read More
Chicago: Zan dangana idan Kotun Ƙoli ta tsarkake Tinubu – Atiku

Chicago: Zan dangana idan Kotun Ƙoli ta tsarkake Tinubu – Atiku

*Ɗan takarar PDP ya ce ba don kansa yake wa Tinubu tone-tone ba*Siyasarka ta zo ƙarshe – APC ga Atiku*Ba na tsoro domin Buhari ya gama kassara kasuwancina a Nijeriya, inji Atiku Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Ɗan takarar babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya kuma tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya yi iƙirarin cewa, idan har Kotun Ƙolin Nijeriya ta yanke hukuncin cewa, Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu tsarkakke ne shi, duk da satifiket ɗin da shi Atikun ya amso daga Jami’ar Chicago dake Birnin Ilinious, don ƙalubalantar sahihancin zaɓensa a 2023, to zai dangana ya haƙura…
Read More
Tawagar UAE ta gana da Tinubu domin ƙara haɗa hulɗar ƙasashen biyu

Tawagar UAE ta gana da Tinubu domin ƙara haɗa hulɗar ƙasashen biyu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tawagar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) ta isa Abuja domin kammala tattaunawa kan yiwuwar ɗage takunkumin hana bai wa 'yan Nijeriya bizar shiga ƙasar. Tawagar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa wacce ta ƙunshi jami’an jihohi irinsu Alshehhu Rasheed, Teo Teck San, Almannaei Khalid, Alhosani Talal, da Janahi Asma sun isa Nijeriya a ranar Lahadi. Tawagar da ake sa ran za ta gana da shugaba Bola Ahmed za ta kuma tattauna batun fara zirga-zirgar jiragen sama tsakanin ƙasashen biyu. Idan za a iya tunawa, UAE a shekarar 2022, ta janye kamfanoninta na jiragen sama, Emirates da Etihad Airways, daga aiki…
Read More
Mutane takwas sun mutu a hatsarin jirgin ruwa a Kebbi

Mutane takwas sun mutu a hatsarin jirgin ruwa a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Bayanai daga garin Yawuri da ke Jihar Kebbi sun bayyana cewa aƙalla mutane takwas ne suka rasu a wani hatsarin jirgin ruwa da ya afku a garin Yawuri farkon makon nan. Wani jami'in hukumar kula da harkokin ruwa ya bayyana wa Wakilin Blueprint Manhaja cewa, jirgin mai ɗauke da mutane kimanin 30 da ya taso daga Agwara da ke jihar Neja ya ɗauko fasinja daga ƙauyukan Gebbe, Kasabo da kuma Mago maƙare da buhunan abinci kimanin tamanin da kaya da dabbobi daga jihar Neja zuwa Yawuri wajen cin kasuwa inda ya kife. Shugaban ƙaramar…
Read More
Mu taimaki Minista Malagi

Mu taimaki Minista Malagi

Masu hikimar magana su na cewa duk wadatar mutum za a iya taimakon sa, haka duk talaucin mutum zai iya taimakon wani. Shi taimako ya danganta daga mutum zuwa wanda zai ma taimakon wani addu'a ce za a taya masa. Wani kuɗi ne, buƙatar wani kuma abin yi ne, buƙatar duka dai mu lura da yadda sabon minista na ɓangaren labarai Alhni Muhammed Idris Malagi ya zamo mai ayukka da yawa, kai ka ce baya ga minista a ɓangaren labarai da kuma wayar da kai, tamkar shi ne mai magana a madadin shugaban ƙasa Tinubu. Duk wanda ya ke sauraren…
Read More
Son zuciya da ɓacin zuciya sai Nijeriya

Son zuciya da ɓacin zuciya sai Nijeriya

Shugabanni suna son su rayu su arzuta cikin walwala, amma basu son talaka ya rayu ya arzuta, shi yasa suke son haifar da ruɗani a fannin tattalin arziki a ƙasa. Allah Ya yi ruwan man fetur a Nijeriya, ya yi albarkar noma da albarkatun ma'adinai da mashigin ruwa da iyakokin ƙasa masu albarka, da kasuwa kala-kala da arzikin jama'a. Amma ƙarfi da yaji ake son a lalata ƙasar a jefata cilkin ruɗani saboda son zuciyar mutane ƙalilan. Saboda duk inda talauci da yaudara da rashin iya jagoranci suka yi katutu dole hassada da rashin martaba juna su shigo daga nan…
Read More