07
Oct
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattijai ta matsa ƙaimi domin gudanar da bincike kan kashe-kashe da ɗaure ‘yan Nijeriya sama da 250 a ƙasar Habasha. Hakan ya biyo bayan wani ƙudiri mai taken, ‘Akwai buƙatar a gaggauta bincike kan kashe-kashen da aka yi wa ‘yan Nijeriya sama da 250 a ƙasar Habasha ba bisa ƙa’ida ba, wanda shugaban marasa rinjaye, Sanata Simon Mwadkwon, ɗan Jam’iyyar Peoples Democratic Party, (PDP) mai wakiltar Filato ta Arewa, da Sanata Victor suka ɗauki nauyi. Da yake gabatar da ƙudirin, Mwadkwon ya buƙaci majalisar dattijai da ta umurci kwamitocin ƙasashen waje da su…
