Editor

9513 Posts
Gwamnan Zamfara ya buƙaci a maida hanyar Funtua-Gusau ta zama tagwaye

Gwamnan Zamfara ya buƙaci a maida hanyar Funtua-Gusau ta zama tagwaye

Daga BASHIR ISAH Gwamna Duada Lawal na Jihar Zamfara, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta samar da tagwayen hanyoyi a hanyar Gusau zuwa Funtua domin bunƙasa cigaban jihar. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da mai magana da yawun Gwamnan, Nuhu Salihu, ya fitar ranar Litinin a Gusau, babban birnin jihar. Gwamna Lawal ya yi wannan kira ne a lokacin da ya kai ziyarar aiki wa Babban Sakataren Ma'aikatar Ayyuka ta Tarayya, Mamuda Mamman, a ofishinsa. Ya ce hakan ɓangare ne na alƙauran da ya yi wa talakawansa a lokacin neman zaɓe. Ya ƙara da cewa, mayar da…
Read More
Shugaba Tinubu ya rushe hukumomin gudanarwa na ma’aikatun gwamnati

Shugaba Tinubu ya rushe hukumomin gudanarwa na ma’aikatun gwamnati

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya amince da rushe duka hukumomin gudanarwa na ma'aikatu da cibiyoyin Gwamnatin Tarayya haɗi da na kamfanoni mallakar gwamnatin. Tinubu ya yi hakan ne domin sauke nauyin da Kundin Tsarin Mulki ya ɗora masa don amfanin al'umma. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Darktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ya fitar. Sanarwar ta ce rushewar ta fara aiki ne nan take ba da ɓata lokaci ba. "Sai dai rushewar ba ta shafi hukumomi da cibiyoyin da ke lissafe cikin Zubi na Uku, Kashi na 1, Sashe…
Read More
Tinubu ya naɗa Nuhu Ribaɗu da wasu a shugabancin fannin tsaro

Tinubu ya naɗa Nuhu Ribaɗu da wasu a shugabancin fannin tsaro

Daga BASHIR ISAH A ranar Litinin Shugaban Ƙasa sauke duka jami'an da ke jan ragamar fannin tsaron Nijeriya nan take. Kazalika, ba tare da ɓata lokaci ba Tinubun ya amince da naɗin waɗanda za su maye gurbin saukakkun. Waɗanda sabbin naɗe-naɗen ya shafa sun haɗa da: 1 Malam Nuhu Ribadu, Mai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Sha'anin Tsaro2 Manjo Janar C.G Musa, Babban Hafsan Tsaro3 Manjo T. A Lagbaja, Babban Hafsan Sojoji4 Rear Admirral E. A Ogalla, Babban Hafsan Sojojin Ruwa5 AVM H.B Abubakar, Babban Hafsan Mayaƙan Sama6 DIG Kayode Egbetokun, Muƙaddashin Sufeto-Janar na 'Yan Sanda7 Manjo Janar EPA Undiandeye,…
Read More
Tinubu ya sauke shugabannin tsaro

Tinubu ya sauke shugabannin tsaro

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sauke shugabannin tsaron Nijeriya baki ɗaya. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Willie Bassey, ya fitar a ranar Litinin. Tinubu ya bi bayan sauke jami'an da naɗa sabbin da za su maye gurbinsu. A cewar sanarwar, “Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya amince da ritayar dukkan shugabannin tsaro da Sufeto-Janar na 'Yan Sanda, masu ba da shawara da Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam." Sanar ta ƙara da cewa, sauke su ɗin ya fara aiki ne nan take, haka ma waɗanda aka naɗa…
Read More
Majalisa: ’Yan amshin shata sun samu ’yan amshi?

Majalisa: ’Yan amshin shata sun samu ’yan amshi?

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Ba wani babban dalili ne ya sa a ke ayyana masu rawa da bazar wasu ko waɗanda ba su da ra’ayin kan su a matsayin ’yan amshin shata ba sai don yadda marigayi Dokta Mamman Shata ke waƙarsa a na yi ma sa amshi ba ragi ko kari. Akwai ma wata waƙar Shata da komai ya ce sai ’yan amshi su ce “HAKANAN NE MAMMAN SHATA IDI ƊAN YELWA.” Duk da ba labarin Shata na ke son yi a nan ba amma haƙiƙa an shan shaharar Shata da baiwar da Allah ya yi ma sa ta…
Read More
Hukumar hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya ta haramta hada-hadar kuɗaɗen intanet na Binance

Hukumar hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya ta haramta hada-hadar kuɗaɗen intanet na Binance

Daga AMINA YUSUF ALI Matakin na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na intanet. Hukumar hada-hadar hannayen jari ta ƙasar ta ce kamfanin na Binance bai yi rajista da ita ba, a don haka ne ta ce ta haramta ayyukan kamfanin a faɗin ƙasar nan. Sanarwar ta kuma gargaɗi 'yan ƙasar da ke mu'alama da kamfanin da su dakata, in ba haka ba kuwa duk abinda ya same su to su kuka da kansu. Sanarwar ta ci gaba da cewa ''An nusar da hukumar kula da hada-hadar hannayen jari ta Najeriya game da shafin…
Read More
Nijeriya ta sake ƙwato kambunta na ƙasar da ta fi zarra a samar da man fetur a Afirka

Nijeriya ta sake ƙwato kambunta na ƙasar da ta fi zarra a samar da man fetur a Afirka

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai ƙasar Nijeriya ta sake yi wa ƙasar Angola fintinkau a matsayin ƙasa mai samar da mafi yawan man fetur a Afirka. Wato kenan ta sake ƙwato kambunta wanda aka santa da shi a baya a matsayin ƙasar da ta fi kowacce samar da man fetur a Afirka. Wannna bayani yana ƙunshe ne a wani jawabi da ƙungiyar ƙasashe masu samar da man fetur (OPEC) rmta saki game da samar da ɗanyen man fetur a cikin watan Mayun 2023. Amma a watan Afrilu ƙasar Angola ta kere Nijeriya wajen samar da man fetur…
Read More
Ya kamata mu san muhimmancin kanmu matasa

Ya kamata mu san muhimmancin kanmu matasa

Assalamu alaikum, kamar yadda na saba aiko da wasiƙu na duk mako a wannan jarida mai albarka, yau ma na zo da wata babbar wasiƙa na kira ga matasa, domin tabbas matasa na da muhimmancin gaske a kowace al’umma, tasirinsu ya fi gaban a zura ido kawai ga al’amura ko yanayin yadda suke gudanar da rayuwa sakaka. Wajibi ne da ya hau kan al’umma ta yi tattalin rayuwar matasa, samar da hanyoyin shigar da saƙonnin abubuwa masu kyau don su siffantu da su, haka kuma a yi musu bayanin illolin abubuwa marasa kyau don su ƙaurace musu. Duk wata ƙasa…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe basarake da ‘ya’yansa huɗu a Kaduna

‘Yan bindiga sun kashe basarake da ‘ya’yansa huɗu a Kaduna

Daga WAKILINMU Wasu da ake zargin 'yan bindiga ne sun kashe Arɗon Birni da Kewaye na Masarautar Zazzau, wato Alhaji Shuaibu Mohammed tare kuma da wasu 'ya'yansa huɗu. Lamarin ya faru ne ranar Asabar da daddare a ƙauyen Dorayi da ke Ƙaramar Hukumar Zaria, Jihar Kaduna. Jaridar Daily Trust ta rawaito cewar, 'yan bindigar kimanin su biyar, sun kuma yi awon gaba da shanu 100 mallakar basaraken. Matar marigayin, Malama Halima Shuaibu, ta faɗa wa manema labarai cewa maharan sun harbi magidan nata ne da bindiga a kai wanda hakan ya yi ajalinsa nan take. Matar ta ce, “An fito…
Read More
Layin lantarki na Shiroro-Kaduna ya lalace – KEDCO

Layin lantarki na Shiroro-Kaduna ya lalace – KEDCO

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki na KEDCO, ya yi ƙarin haske dangane da ƙarancin wutar lantarki da ake fuskanta a jihohin Kano da Katsina da kuma Jigawa. Kamfanin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi wadda shugaban sashen yaɗa labaran kamfanin, Sani Bala Sani, ya sanya ma hannu ta ce, lamarin ya faru ne sakamakon lalacewar layin wutar na Shiroro-Kaduna 330KV. Kamfanin ya bayyana cewa tuni dai TCN ta fara aikin gyaran layin wutar wanda ake saran kammalawa a jiya lahadi. Daga ƙarshe ya bai wa al'umma haƙuri tare da bada tabbacin…
Read More