07
Apr
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta gurfanar da kamfanin Binance Holdings Limited da manyan jami’anta biyu, Tigran Gambaryan da Nadeem Anjarwalla da ya gudu a gaban kotu bisa zargin ƙin biyan haraji. An gurfanar da kamfanin da shugabannin biyu a gaban mai shari’a Emeka Nwite na babbar kotun tarayya da ke Abuja. Ɗaya daga cikin waɗanda ake tuhumar Tigran Gambaryan ya isa kotun ne da misalin qarfe 9:15 na safiyar ranar Alhamis yayin da abokin aikinsa, Anjarwalla ba ya nan saboda an ce yana gudu. Waɗanda ake tuhumar dai suna fuskantar tuhume-tuhume biyar na halasta kuɗaɗen haram, da…
