06
Apr
Daga UMAR AƘILU MAJERI a Dutse Gwamna Jihar Jigawa Umar Namadi, ya dakatar da Kwamishinan Harkokin Kasuwanci na Jihar, Hon Aminu Kanta, bisa zargin karkatar da kuɗaɗen jama'a. Ana zargin Aminu Kanta da wawushe kuɗaɗen da gwamnatin jihar ta ware domin tallafa wa al'ummar Ƙaramar Hukumar Ɓabura da abinci a lokacin azumin watan Ramadan. Bayanin dakatarwar na ƙunshene a cikin wata takardar sanarwa mai ɗauke da sa hannun Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Alhaji Bala Ibrahim Mamsa wadda aka raba wa manema labarai. Sanarwar ta ce gwamnatin Jihar ta dakatar da Aminu Kanta daga muƙaminsa na Kwamashinan Harkokin Kasuwancin Jihar Jigawa…
