05
Apr
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Makiyaya a Ƙaramar Hukumar Bokkos da ke Jihar Filato, sun koka cewa ɓarayin shanu sun arce musu shanu sama da 390 da kudin su ya kai aƙalla Naira miliyan 300. Makiyayan sun ce an yi awon gaba da shanun a lokacin da suke kiwo a Bot, Faranti, Anguwan Abuja, Makada da Wumat. Manhaja ta buga cewa shugaban ƙungiyar ci gaban Fulani na ‘Gan Allah’ dake qaramar hukumar Bokkos Saleh Adamu ya ce sun kai ƙarar abinda aka yi musu zuwa ga kwamandan sashin ‘Operation Safe Haven’ da ke yankin. “A ranar 4 ga Maris,…
