Editor

9513 Posts
Anka ya zama shugaban ƙungiyar Hausa ta BUK

Anka ya zama shugaban ƙungiyar Hausa ta BUK

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Fitaccen marubucin littattafan Hausa da finafinan Kannywood, Malam Kabiru Yusuf Fagge wanda aka fi sani da ANKA ya zama shugaban ƙungiyar Hausa ta Jami'ar Bayero da ke Kano, a wani zaɓe da ƙungiyar ta gudanar ranar Jumma'ar da ta gabata 22 ga watan Maris, 2024 a zangon karatu na 2022/2023. Marubucin wanda yake ɗalibta a Sashin Nazarin Harsunan Najeriya, inda yake karatun digirinsa na farko a fannin Harshen Hausa, ya zama shugaban ƙungiyar ne bayan zaven da aka yi masa tare da wasu masu dafa masa su goma sha ɗaya. Da suka haɗa da shi, Kabiru…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya rattaɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu

Daga BASHIR ISAH A ranar Laraba Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya rataɓɓa hannu kan Dokar Bai wa Ɗalibai Rancen Karatu ta 2024. Da wannan, sabuwar dokar za ta fara aiki ke nan, inda za ta bai wa ɗalibai a manyan makarantu zarafin samun rance daga gwamnati domin gudanar da harkokin karatunsu. Tinubu ya sanya wa dokar hannu ne bayan da Majalisar Tarayya ta nazarci rahoton Kwamitin Kula da Manyan Makarantu da kuma asusun TETFund.
Read More

Allah ya jiƙan Gumi babba da Gumi ƙarami

Daga ALI ABUBAKAR SADIQ Sheikh Abubakar Mahmud Gumi, Allah Ya rahamshe shi, uba ne gare ni sakamakon kasancewarsa aboki na ƙut-da-ƙut ga mahaifina. Sun yi karatu tare kuma sun fito daga yanki guda, sunayensu guda, ɗaya mutumin Gumi xaya kuma mutumin Furfuri. Allah ya sada su da rahamarsa. A shekarar 1989, na yi tattaki daga Kano zuwa Kaduna har gidan Malam Abubakar Gumi da ke Modibbo titin Adama Street, inda na samu ganin sa, na gabatar da kaina domin bai san ni a zahiri ba, sannan na miqa masa buƙatata, ya yarda ya sa min hannu na ya zame min…
Read More
Gwamnatin Zamfara ta kafa dokar taƙaita zirga-zirga a wasu sassan jihar

Gwamnatin Zamfara ta kafa dokar taƙaita zirga-zirga a wasu sassan jihar

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Jihar Zamfara ta kafa dokar taƙaita zirga-zirga a yankunan da take iyaka da jihohin Katsina da Sakkwato a matsayin ɓangare na yaƙi da matsalolin tsaron da suka addabi ƙasar. Dokar za ta fara aiki ne daga ƙarfe na 7:00 na dare zuwa 6:00 na safe. Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al'adu na Jihar, Manir Haidara, shi ne ya bayyana haka a ranar Talata. Haidara ya ce dokar na daga shawarwarin da Majalisar Tsaron jihar ta bayar a wajen taronta. A cewar Kwamishinan, “Daga yau, gwamnatin jihar ta ba da odar taƙaita zirga-zirga a yankin Yankara kan iyakar…
Read More
Yanzu-yanzu: Gwamnati ta ƙara kuɗin wutar lantarki

Yanzu-yanzu: Gwamnati ta ƙara kuɗin wutar lantarki

Daga BASHIR ISAH Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC) ta ba da umarnin gaggawa kan ƙarin kuɗin wutar lantarki daga ranar Laraba, 3 ga watan Afrilun da ake ciki. Mataimakin Shugaban hukumar NERC, Musiliu Oseni ne ya bayyana haka ga manema labarai ranar Laraba a Abuja. Oseni ya ce ƙarin ya shafi kashi 15 na adadin masu amfani da wutar lantarki ne wanda kuma su ne ke shan kashi 40 na wutar da ake samarwa baki ɗaya. Ko a watan Janairun da ya gabata, NERC ta ce gwamnatin Nijeriya za ta biya Naira tiriliyan 1.6 don tallafa wa…
Read More
A kawo ɗauki don magance tsadar kuɗin zuwa aikin hajjin bana

A kawo ɗauki don magance tsadar kuɗin zuwa aikin hajjin bana

Daga ABUBAKAR IBRAHIM A kowace shekara, al'ummar Musulmi suna gudanar da aikin Hajji domin cika ɗaya daga cikin shikashikan addininsu guda biyar. Abu ne wanda kowane Musulmi ke son cimmawa, aqalla sau ɗaya a rayuwarsa, yayin da kuma wani mai ƙumbar susa yake da burin ya sake komawa ya ƙara yi. Duk da haka, wanda ke da hali ne kaɗai aka wajabta wa yin wannan tafiya zuwa ƙasa mai tsarki don sauke farali. A Nijeriya, tuni shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2024 suka kankama. Sai dai kuma ana ta samun wani babban ƙalubale, musamman na kuɗin tafiya aikin na…
Read More
Matan aure barka da Ramadan! (2)

Matan aure barka da Ramadan! (2)

Tare da AMNINA YUSUF ALI Assalamu alaikum, uwargida da kuma amarya. Ina yi muku sannu da ibada a wannan wata mai alfarma. Fatan Allah ya ba mu dacewa a cikinsa. Har yanzu dai muna kan maudu'in nan namu na sanar da girke-girke ga mata masu aure saboda shigowar watan Ramadan mai albarka domin su sauya wa Maigida samfurin tukunya domin samun ninkin ƙarin lada da watan Ramadan watan rahma da yafe zunubai da ɗaga darajar bayi tare da amsa dukkan buƙatu. Allah ya yi mana katari da dukkan romo da falaloli da suke a wannan wata. Kuma Allah ya nuna…
Read More
‘Yan bindiga sun sace wasu masallata a Gusau

‘Yan bindiga sun sace wasu masallata a Gusau

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau ’Yan ta’addan masu tayar da ƙayar baya sun mamaye yankin Samaru da ke Gusau, babban birnin jihar Zamfara, inda suka yi garkuwa da ɗimbin masu gudanar da ibadar Sallar Tahajjud da tsakar daren ranar Talata. Mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa wakilinmu cewa ‘yan bindigar sun kewaye masallatan da misalin ƙarfe 1:30 na daren yau Talata, inda suka far wa masu ibada a cikin masallacin tare da yin garkuwa da dama daga cikinsu. "Kamar yadda nake magana a yanzu, har yanzu ba mu kai ga tantance adadin waɗanda aka yi…
Read More
An gano gawar DCP a gidansa a Oyo

An gano gawar DCP a gidansa a Oyo

Daga BASHIR ISAH An gano Mataimakin Kwamishinan 'Yan Sanda (DCP), Gbolahan Olugbemi, kwance a mace a gidansa da ke Ogbomosho, Jihar Oyo. MANHAJA ta tattaro Olugbemi, wanda ke aiki da rundunar 'yan sanda ta Jihar Legas, ya tafi gida ne don yin hutun Easter. An ce mutuwar jami'in cike take da mamaki da ruɗani wanda hakan ya jefa jami'an sashen bincike na FCID na Legas cikin halin jimami. Majiyarmu ta rawaito cewa, Kakakin FCID, ASP Aminat Mayegun, ta ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano dalilin mutuwar jami'in. Majiya ta kusa da FCID ta ce za a gayyato…
Read More
Gobara ta ƙone shaguna da dama a Kwara

Gobara ta ƙone shaguna da dama a Kwara

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga Jihar Kwara sun ce shaguna da dama sun ƙone tare da asarar dukiya mai yawa sakamakon ƙobarar da ta auku a Kasuwar Owode da ke garin Offa a jihar. An ce gobarar ta fara ne da asubahin Talata wanda hakan ya yi sanadiyar ƙonewar wasu shaguna a kasuwar. Cikin wani faifan bidiyo na gobara wanda aka yaɗa an jiyo murya cikin harshen Yarabanci na cewa: “Wutar ta yi ƙarfi sosai, ba lantarki ya haifar da gobarar ba, wataƙila sakamakon girki da ake yi kusa da wurin ne." Bayanai sun daga bisani, Jami'an Kwana-kwana na ji…
Read More