Editor

9513 Posts
An kashe mai juna biyu a turmutsutsun sayen shinkafar Kwastom

An kashe mai juna biyu a turmutsutsun sayen shinkafar Kwastom

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mutane bakwai, ciki har da mace mai juna biyu sun rasu a yayin turereniyar sayen shinkafar da Hukumar Kwastam ta yi gwanjo a kan N10,000 kowane ƙaramin buhu a Jihar Legas. Wasu da dama kuma sun jikkata a turereniyar da ta barke a lokacin da wasu bata-gari suka yi yunƙurin shiga ofishin hukumar da ke gwanjon shinkafar da ƙarfin tuwo. Lamarin ya faru ne ranar Juma’a da hukumar ta fara gwanjon shinkafar a ofisinta da ke yankin Yaba. Gwanjon shinkafar da hukumar ke yi wani ɓangare na yunƙurinta rage wa ’yan Nijeriya raɗaɗin tsadar…
Read More
MOPPAN ta nuna damuwa kan murabus ɗin Kwamandan Hisba

MOPPAN ta nuna damuwa kan murabus ɗin Kwamandan Hisba

*Ta buƙaci Daurawa ya sake nazari kan matakin da ya ɗauka Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Masu Shirya Fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN) ta nuna damuwarta kan ajiye muƙami da Sheikh Aminu Daurawa ya yi a matsayin Kwamandan Hukumar Hisba ta Jihar Kano. MOPPAN ta ce Daurawa ya ajiye muƙamin nasa ne bisa dalilin rashin ƙwarin gwiwa daga ɓangaren Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf. Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a cikin sanarwar da ta fitar a ranar Juma'a mai ɗauke da sa hannun Sakataren Hulɗa da Jama'a na Ƙasa, Al-Amin Ciroma. MOPPAN ta bakin Shgugabanta na Kasa, Habibu Barde, ta ce tana…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Shugaban Hisbah, Sheikh Daurawa ya ajiye muƙaminsa

Da Ɗumi-ɗumi: Shugaban Hisbah, Sheikh Daurawa ya ajiye muƙaminsa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Hukumar Hisbah a Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya sanar da ajiye muƙaminsa a matsayin Babban Kwamandan Hisbah, tare da nuni davrashin ƙwarin gwiwa daga ɓangaren Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf. Daurawa ya ce duk da ƙoƙarin da yake yi wajen kyauta tarbiyya a jihar a matsayinsa na shugaban Husbah, amma cewa ya karaya da yanayin kamalaman gwamnan. Faifan bidiyonnya ya yaɗa a shafinsa na soshiyal midiya, Malamin ya ce, "Yanzu haka ina Jihar Kaduna ina ganawa da 'yan majalisa ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar don tattauna aiwatar da dokar yin gwaji kafin aure a Kano…
Read More
Gwamnatin Zamfara ta yi wa marasa lafiya 2,213 magani kyauta

Gwamnatin Zamfara ta yi wa marasa lafiya 2,213 magani kyauta

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal, ta ce ta yi wa 'yan jihar su 2,213 magani kyauta albarkacin shirinta na kula da lafiya kyauta da take gudanarwa. Gwamnatin ta ce kawo yanzu ta kammala kashi na uku na shirin wanda aka samar domin kyautata lafiyar 'yan jihar musamman masu fama da rashin lafiya. Wannan bayani na ƙunshe ne cikin sanarwar da mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris ya fitar a ranar Alhamis. Sanarwar ta ce kashi na uku na shirin ya gudana ne daga ranar 23 zuwa 25 na Fabrairun 2024. “Gwamnatin Gwamna…
Read More
Gwamnati ba za ta yi amfani da rahoton Oronsaye don ta kori ma’aikata ba – Minista Idris

Gwamnati ba za ta yi amfani da rahoton Oronsaye don ta kori ma’aikata ba – Minista Idris

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Zartaswa ta Ƙasa ta yanke shawarar yin amfani da rahoton yi wa ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya garambawul na kwamitin Steve Oronsaye, domin a rage yawan kashe kuɗaɗe wajen tafiyar da ayyukan gwamnati. Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris ne ya bayyana haka a ƙarshen taron majalisar a ranar Litinin, a Abuja. Idris ya ce wasu Ma’aikatun da Sassa da Hukumomi da Cibiyoyi za a rushe su, za a haɗe wasu da wasu, wasu kuma za a maida su cikin hukumomin gwamnati da suka cancanta. Sai dai Idris ya ce…
Read More
Ƙudirina shi ne inganta Hukumar Kula da Ilimin Kimiyya da Fasaha a Kano – Farfesa Ɗahiru Saleh

Ƙudirina shi ne inganta Hukumar Kula da Ilimin Kimiyya da Fasaha a Kano – Farfesa Ɗahiru Saleh

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Shugaban Hukumar Kula da Ilimin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, Farfesa Ɗahiru Saleh Muhammad, ya bayyana cewa babban burinsa shi ne inganta ayyukan hukumar kimiyya da fasaha ta Jihar Kano a mastayinsa na masani akan harkar ilimin kimiyya da fasaha. Don haka ya ce ƙudirinsa shi ne ɗaukaka darajar hukumar da kuma yin aiki bisa ƙa'idar koyar da ilimin kimiyya da fasaha domin kwalliya ta biya kuɗin sabulu wato kowacce ƙwarya a ajiyeta a gurbinta, kamar yadda ƙudirin gwamnan Kano ya ke Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya ke na bunƙasa ilimin kimiyya da fasaha…
Read More
Yadda ‘yan bindiga suka banka wa gidaje, asibiti da ofishin ‘yan sanda wuta a Katsina

Yadda ‘yan bindiga suka banka wa gidaje, asibiti da ofishin ‘yan sanda wuta a Katsina

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ranar Litinin ce bayan sallar magriba, gungun ‘yan bindiga akan babura suka afka cikin garin Wurma, a Ƙaramar Hukumar Kurfi. Maharan sun banka wa ofishin ‘yan sanda da wani sabon asibitin kula da marasa lafiya wuta. Haka kuma sun banka wa gidajen mazauna garin wuta da dama. ‘Yan bindigar sun kuma ƙone motoci duk a cikin daren. Mazauna garin sun tabbatar wa wakilin mu cewa sun arce da mutum 12. Wata majiya ta shaida wa wakilin mu cewa maharan sun afka wa garin Wurma da ke yamma da Birchi su na kan babura, ƙoƙarin…
Read More
Teku ta ci matashi a Legas

Teku ta ci matashi a Legas

Daga BASHIR ISAH Rahotannai daga Jihar Legas sun ce, teku ya yi gaba da wani matashi ɗan shekara 13, mai suna Kelvin Onyengba, a lokacin da suka je shaƙatawa tare da abokansa a bakin teku a yankin Ajah da ke Legas. Majiyarmu ta ce lamarin ya auku ne ranar Talata da rana. Bayanai sun ce igiyar ruwa ce ta ja matashin zuwa cikin teku a daidai lokacin da suke wanka tare da wasu abokansa su biyar. Majiya ta ce, "Mahaifiyar yaron ta ce igiyar ruwa ce ta ja ɗanta. Sun tafi shaƙatawa ne a bakin teku tare da wasu abokansa…
Read More
Mazauna Chikun sun yi zanga-zanga kan harin ta’addanci a yankinsu

Mazauna Chikun sun yi zanga-zanga kan harin ta’addanci a yankinsu

Daga BASHIR ISAH Mazauna yankin Chikun cikin Ƙaramar Hukumar Goningora da ke Jihar Kaduna sun tare babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna a yankinsu sakamakon zanga-zangar da suka gudanar a ranar Alhamis. Jaridar Intelrigeon ta rawaito cewar, mazauna yankin sun shirya zanga-zangar ne domin nuna rashin jin daɗinsu da harin ta'addancin da 'yan bindiga suka kai yankin. Zanga-zangar ta yi sanadiyar hana abubuwan hawa zirga-zirga a hanyar kamar yadda aka saba. A cewar tashar Channels TV, mazauna yankin da dama ne aka yi awon gaba da su yayin da wasu sun jikkata sakamakon harin 'yan bindiga a yankin a ranar Laraba.…
Read More
Lawal ya ƙaddamar da raba kayayyakin karatu ga makarantu 250 a Zamfara

Lawal ya ƙaddamar da raba kayayyakin karatu ga makarantu 250 a Zamfara

Daga BASHIR ISAH Gwanna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada cewa fannin ilimi shi ne kan gaba a jerin ɓabgarorin da zai bai wa fifiko wajen gina jihar Zamfara. Lawal ya bayyana haka ne a wajen bikin ƙaddamar da raba kayayyakin koyo da koyarwa ga makarantu wanda ya gudana ranar Laraba a Gusau, babban birnin jihar. Rabon kayayyakin ya shafi makarantun gwamnati 250 ne da suka haɗa firamare da ƙananan sakandare a jihar. Mai magana da yawun Gwamna, Sulaiman Bala Idris ya ce, Hukumar Ilimin Bai-ɗaya (UBEC) da ke Abuja da kuma UNICEF su ne suka samar da kayayyakin.…
Read More