Editor

9513 Posts
Idan ka ga marubuci yana rubutu ba ya samun kuɗi shi ya so – Sadik Lafazi

Idan ka ga marubuci yana rubutu ba ya samun kuɗi shi ya so – Sadik Lafazi

"Wasu ƙungiyoyin ba sa son ɗaukar sabon marubuci" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Baƙon marubucin mu na wannan mako shi ne Malam Sadik Abubakar Abdullahi, shugaban ƙungiyar Lafazi Writers Association, ɗaya daga cikin fitattun ƙungiyoyin marubuta na onlayin da suke taka rawar gani wajen fitar da littattafai masu ƙunshe da basira da darussa masu yawa, da kuma kiyaye ƙa'idojin rubutun Hausa. Ya kasance daga cikin maza marubuta da suka zama tamkar madubi ko ababen koyi ga matasan marubuta masu tasowa. A zantawarsa da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya bayyana masa yadda yadda shi da wasu marubuta suka kafa ƙungiyar…
Read More
Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu tsige wasu manyan jami’ansa

Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu tsige wasu manyan jami’ansa

Daga BASHIR ISAH Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar mata ta neman tsige Mataimakin Babban Jami'in Hukumar FCCPC, Barrister Babatunde Irukera. Wasiƙar da Tinubun ya aike wa Majalisar wadda Shugaban Majalisar ya karanto ta yayin zaman Majalisar a ranar Laraba, ta nuna Tinubu ya buƙaci tsige Irukera ne saboda rashin kataɓus. Dokar FCCPC ta tanadi cewa, sai da sahalewar Majalisar Dattawa kafin Shugaban Ƙasa zai iya tsige Mataimakin Babban Jami'in Hukumar. Sanarwar da ta nuna tsige Irukera ta sake nuni da yadda Tinubu ya tsige Babban Daraktan hukumar Bureau of Public Enterprises (BPE), Alex…
Read More
A da neman albarkar aure ya fi yawa a zukatan mutane fiye da yawan lefe – Saliha Zariya

A da neman albarkar aure ya fi yawa a zukatan mutane fiye da yawan lefe – Saliha Zariya

*Lefe yana da kyau, muddin aka karve shi a yadda ya zo - Fatima Ɗanborno Daga AISHA ASAS Kamar yadda muka sani, shafin Gimbiya shafi ne na musamman da ke faɗakar da mata ta ɓangarori da dama, tare kuma da bayyana haƙoƙƙinsu da kuma ilimitar da su kan abinda ya shafi rayuwarsu da kuma zamantakewar aure. Don haka ne ma shafin bai tsaya a iya fira da mata don jin rayuwarsu da hanyoyin da suka bi don samun cigaba tare da ƙalubalen da suka fuskanta don ya zama wata makaranta ga sauran mata ba, domin mukan zaƙulo muhimman ababe ko…
Read More
Kada mu cire tsammani da gyaruwar ƙasar nan

Kada mu cire tsammani da gyaruwar ƙasar nan

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Kwanakin baya na samu damar halartar wani babban taron wayar da kai na matasa, wanda wata ƙungiyar matasan Jihar Gombe mai laƙabi da TedX Pantami ta shirya da nufin tattauna wasu matsaloli da suka addabi al'ummar Arewa, musamman mazauna Jihar Gombe. Har wa yau kuma a samar da mafita wanda gwamnati da al'umma za su yi aiki da su, don samar da canji a rayuwarsu. Taron, wanda ya sa mu halartar manyan manazarta, malaman jami'o'i, da awararru a ɓangarori daban-daban, da suka haɗa da ɓangaren lafiya, ilimi, da zamantakewa. Kuma kowannensu ya gabatar da laccoci…
Read More
Za a yi taron wayar da kan ‘yan Kannywood kan sabbin dokokin Hukumar NCC – KSCB

Za a yi taron wayar da kan ‘yan Kannywood kan sabbin dokokin Hukumar NCC – KSCB

Hukumar kare haƙƙin masu mallaka tare da yaki da satar fasaha ta kasa (NCC), ta nemi haɗa hannu da Hukumar tace Fina-finai da Ɗab'i ta Jihar Kano domin wayar da kan abokan hulɗarsu kan sabbin dokokin hukumar da waɗanda aka yi wa gyara. Da yake jawabi a yayin ganawar sa da manema labarai, Alh Sani Ahmad wanda shi ne mai kula da jihohin Kano, Katsina da Jigawa na Hukumar kula da haƙƙin masu mallaka tare da satar fasaha ta kasa ya ce, ya ziyarci Hukumar ta tace Fina-finan ne a domin neman goyan bayan su ta yadda za su haɗa…
Read More
NLC ta janye ci gaba da zanga-zangar gama-gari

NLC ta janye ci gaba da zanga-zangar gama-gari

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta dakatar da ci gaba da zanga-zangar gama-gari na yini biyun da ta shirya. Ƙungiyar ta sanar da hakan ne a cikin sanarwar bayan taron da ta fitar bayan taron Majalisar Zartarwar ƙungiyar, tana mai cewa zanga-zangar ranar farko ta haifar da cigaba mai ma'ana. Don haka ta je ta janye ci gaba da zanga-zangar a rana ta biyu biyo bayan nasarar davta samu a ranar farko ta zanga-zangar. Da fari NLC ta ƙeƙashe ƙasa inda ta ce babu gudu babu ja da baya game da zanga-zangar yini biyun da ta shirya…
Read More
Lawal zai gina garejin manyan motoci a sassan Zamfara

Lawal zai gina garejin manyan motoci a sassan Zamfara

Daga BASHIR ISAH Gwamna Jihar Zamfara Dauda Lawal, ya bayyana cewa zai gina wuraren hada-hadar motocin kasuwa a Zamfara a matsayin ɓangaren ƙudirinsa na raya birane a jihar. Lawal ya furta hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin ƙungiyar masu motocin haya ta NARTO da ta direbobin tankokin dakon fetur, PTD. Cikin sanarwar da Kakakinsa Sulaiman Bala Idris ya fitar, Gwamna Lawal ya ce, “Na ba da umarnin a gina garejin manyan motoci guda biyu, ɗaya a hanyar Funtua zuwa Gusau gudan kuma a hanyar Sokoto zuwa Gusau. "Ni na gayyato NARTO da PTD kan su zo su…
Read More
‘Za mu ci gaba da zanga-zanga’ — cewar NLC

‘Za mu ci gaba da zanga-zanga’ — cewar NLC

*Ganawarsu da gwamnati ba ta haifar da ɗa mai ido ba Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta ce za ta ci gaba da zanga-zangarta tun da ba a cimma maslaha ba a taron da suka yi da Gwamnatin Tarayya a ranar Litinin. Ɓangarorin biyu sun gana ne a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja da zummar lalubo bakin zare dangane da zanga-zangar da NLC ke kan gudanarwar domin nuna rashin jin daɗinta da halin tsadar rayuwar da 'yan ƙasa ke fuskanta. Shugaban NLC na ƙasa, Joe Ajaero, ya ce "Za a ci gaba da zanga-zangar, kuma haƙƙi…
Read More
Rayuwar Sarki Haile Selassie na Habasha

Rayuwar Sarki Haile Selassie na Habasha

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Haile Selassie an haifeshi a ranar 23 ga watan Yuli na shekara ta 1892 a kusa da Harar cikin ƙasar Habasha, inda aka raɗa masa suna da Tafari Makonnen. Mahaifinsa amintacce ne kuma na kusa da Sarki Menelik na II. An kira shi zuwa kotu a Addis Ababa lokacin da babansa ya mutu a 1906. A 1916 ya zama mabiyin aqidar Ras Tafari, da ake zaton ya gaji sarauniya Zauditu da ke zaman 'ya ga Menelik na II. A shekara ta 1928 tare da magoya bayansa sun sanya sarauniyar ta ba shi sarauta. A shekara ta…
Read More
Darasin haƙuri a zamantakewa (3)

Darasin haƙuri a zamantakewa (3)

Daga AMINA YUSUF ALI Barkanku da jimirin karatun Manhaja. A mako da ya gabata mun fara kawo muku da bayanai a game da yadda za a gyara aure ta hanyar yin haƙuri a gidan Malam Bahaushe. Amma fa haƙurin ta ɓangaren masu gida, wato maza. A makon da ya gabata mun fara kawo muku wasu bayanai game da yadda su maza suke ganin su yin haƙuri a zamantakewa ta aure bai kama su ba. Kuma al'umma duk suna neman su amince da haka. Amma a zahirin gaskiya ta fuskar zamantakewa da addini ma ya kamata a ce kowanne ɗan Adam…
Read More