27
Feb
Daga BASHIR A halin da ake ciki, haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta shirya zanaga-zangar lumana a sassan ƙasa domin nuna rashin jin daɗinta game da ƙuncin rayuwar da 'yan ƙasa ke fuskanta. Bayanan da MANHAJA ta kalato a ranar Talata sun nuna an hangi masu zanga-zangar a yankin Ikeja, Jihar Legas. Inda aka ga da damansu ɗauke da kwalaye masu ɗauke da saƙonni daban-daban kamar "A kawo ƙarshen yunwa da talauci yanzu" da dai sauransu. A Jos babban birnin Filato ma haka lamarin yake, a nan ma an ga ɗaruruwan masu zanga-zangar sun mamaye wasu manyan hanyoyin birnin.…
