Editor

9513 Posts
Zancen banza ne ‘yan bindiga ke yi na cewar za su kai mani hari – Raɗɗa

Zancen banza ne ‘yan bindiga ke yi na cewar za su kai mani hari – Raɗɗa

Daga Umar Garba a Katsina Gwamnan jihar Katsina Dakta Dikko Umar Raɗɗa, ya bayyana cewar tun da ya zama gwamnan jihar Katsina ba qaramar hukumar da ta gagare shi shiga saboda tsoron ta'addacin 'yan bindiga a jihar. "Zancen banza ne 'yan bindiga ke yi cewar za su kai mani hari, ba inda ɗan ta'adda zai hana ni zuwa a Katsina, ba kuma hanyar da zai hana ni bi." Inji gwamnan. Raɗɗa na mayar da martani ne lokacin da yake zantawa da majiyar jaridar Manhaja ta DW, game da wani rahoto dake cewa 'yan bindiga na shirin kai ma shi hari…
Read More
Wata biyar ana garkuwa da ’yan matan Zamfara

Wata biyar ana garkuwa da ’yan matan Zamfara

*’Yan bindiga sun nemi a saki babansu, cewar iyayen yaran*Ba ni da masaniya, inji Gwamnan Dauda Daga SUNUSI MUHAMMAD a Gusau A halin da ake ciki yanzu kimanin watanni biyar da suka gabata kenan da wasu ’yan ta’adda suka afka wa gidajen kwanan ɗaliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya da ke Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara, inda suka yi awon gaba da kimanin ɗalibai mata 30 da wasu ma’aikatan kamfanin gine-gine su tara yayin da a halin yanzu kimanin ɗalibai mata 12 suka rage har yanzu babu wani cikakken bayanin akansu. Wakilin Blueprint Manhaja a Zamfara, SANUSI MUHAMMAD, ya yi bincike game…
Read More
Gaza, Amurka ta sake hawa kujerar ta ki

Gaza, Amurka ta sake hawa kujerar ta ki

Tare da NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Zantawa kan yaƙin Gaza na cigaba da zama mai muhimmanci kuma kasancewarsa cikin manyan lamuran da ke ɗaukar hankalin ƙasashen duniya. Dalilin rincavewar fitinar Gaza an daina batun yaƙin nan na Sudan tsakanin shugaban mulkin soja Janar Abdelfatah Burhan da na 'yan sa kai Janar Hameti Hamdan Daglo. Kuma ba wai fitinar ta Sudan ta kare ba ne. Ga yaƙin da Rasha ke yi kan Yukrain inda ƙasashen yammacin duniya ke marawa shugaban Yukrain Volodymyr Zelenskyy baya. Hakiƙa an san shugaban Rasha Vladimir Putin ba zai dakatar da kunce ɗamarar yaƙin ƙasar Yukrain ba don…
Read More
Yadda dillalin jarida ya rikiɗe zuwa shehin malamin jami’a

Yadda dillalin jarida ya rikiɗe zuwa shehin malamin jami’a

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi  An shawarci manema labarai da suke kan ganiyarsu a fagen fama, mazauna Jihar Bauchi da cewar, kowane ɗaya daga cikinsu zai iya ko za ta iya murjewa daga masomi ko tale-tale, cikin sana'arsa/ta ta yaɗa labarai, har ya/ta kai ga cimma muradun sa/ta na rayuwa, walau kan wannan sana'a da yake/take kai, ko wata makamanciya da za ta kai shi/ta ga tudun mun tsira. Wannan shawara ma'abuciyar ƙarfafa zuciya ta fito ne daga bakin wani jigon gwamnatin jihar Kaduna, kuma babba sakatare na sirri wa Gwamnan jihar ta Kaduna, Farfesa Bello Ayuba a kwanakin baya…
Read More
Mun sha alwashin inganta fannin ilimin Zamfara – Lawal

Mun sha alwashin inganta fannin ilimin Zamfara – Lawal

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya bada tabbacin gwamnatinsa ta bada himma wajen samar da ilimi mai nagarta a Zamfara. Ya bayyana hakan ne sa'ilin da yake jawabi a wajen gasar wasannin motasa jiki na bana wadda makarantar Almufida International Academy ta shirya a Gusau, babban birnin jihar. Kakakin Gwamana, Sulaiman Bala Idris, ya ce mamallakin makarantar ya karrama Gwamna Lawal da kambar yabo ta 'Grand Commander of Friends of the College' (GCFC). Da yake jawabi, Lawal ya nuna gamsuwarsa dangane da bajintar da ɗaliban makarantar suka nuna a gasar tare da yaba wa hukumar makaranta…
Read More
Buƙatar samar da ’yan sandan jihohi

Buƙatar samar da ’yan sandan jihohi

Ƙirƙirar 'yan sandan jihohi dai ta kasance batun da ya daɗe ana muhawara a kai a Nijeriya. Bayan kwashe shekaru masu yawa, shugabannin Nijeriya sun samu matsaya kan batun samar da rundunar 'yan sanda jihohi a ƙasar. A makon da ya gabata, Shugaba Bola Tinubu da gwamnonin jihohi 36 suka tattauna kan batun samar da 'yan sandan jihohi don magance matsalolin tsaro da ke barazana ga ƙasar, waɗanda suka haɗa da satar mutane da fashi da makami da suka zama ruwan dare. Ƙudirin samar da 'yan sandan jihohi a Nijeriya ya tsalake karatu na biyu a zauren Majalisar Wakilai domin…
Read More
Tashin kayan masarufi na barazanar durƙusar da kasuwanci – ‘Yan kasuwar Kano

Tashin kayan masarufi na barazanar durƙusar da kasuwanci – ‘Yan kasuwar Kano

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano Gamayyar shugabannin ƙungiyoyin 'yan kasuwar Kano da suka yi wani gangami da kira da gwamnatin Bola Tinubu sun shawarci gwamnatin Njeriya da ta ɗauki matakin gaggawa ko kuma kasuwanci ya durkushe gabaki ɗaya a Nijeriya musamman a wannan lokaci da dala ta haura Naira 1500 kuma ta ke ta hauhawar kamar motar da birkin ta ya tsinke ana gudu a 180 na ma’aunin tuƙin mota. Gamayyar ƙungiyoyin na shugabannin 'yan kasuwar Kano kimanin 30 da suka yi gangami a taron da suka gabatar a ranar Lahadi da ta gabata ƙarƙashin shugabancin shugaban gamayyar ƙungiyoyin 'yan…
Read More
ECOWAS ta ɗage takunkumin da ta ƙaƙaba wa Nijar, Burkina Faso, Mali, Guinea

ECOWAS ta ɗage takunkumin da ta ƙaƙaba wa Nijar, Burkina Faso, Mali, Guinea

ECOWAS ta yanke shawarar ɗage wasu takunkuman da ta ƙaƙaba wa ƙasashen Jamhuriyar Nijar da Mali da Guinea. Ƙungiyar ta cimma wannan matsaya ne a wajen taronta da ta shirya ranar Asabar a Abuja. Sai dai ɗage takunkumin ba na baki ɗaya ba ne, wasu ne daga cikin takunkuman da ECOWAS ɗin ta kafa wa ƙasashen da lamarin ya shafa. Idan ba a manta ba, a watan Janairun da ya gabata Nijar da Mali da Burkina Faso suka sanar da ficewarsu daga ƙungiyar ECOWAS sakamakon takunkuman da aka kafa musu biyo bayan juyin mulkin da ya faru a ƙsashen.
Read More
Gwamnatin Zamfara ta biya miliyan N613 ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya

Gwamnatin Zamfara ta biya miliyan N613 ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Gwamnatin Jihar Zamfara ta biya Naira miliyan 613 ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya daga jihar su 414. Shugaban kwamitin tantancewa kuma babban sakataren ma’aikatar kuɗi ta jihar Muhammad Kabiru Abubakar ne ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a ofishinsa. A cewarsa, kwamitinsa ya karvi bayanai sama da 4000 na waxanda suka amfana. Ya kuma kara da cewa an ɗora wa kwamitin ne domin tabbatar da waɗanda suka yi ritaya daga shekarar 2015 zuwa yau domin su ci gajiyar giratuti. Ya yi alƙawarin yin adalci wajen sauke aikin da aka bai…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe fararen hula takwas a Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe fararen hula takwas a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Aƙalla fararen hula takwas ne ‘yan bindiga suka kashe a Ƙaramar Hukumar Maradun ta jihar Zamfara. Wani mazaunin yankin mai suna Muhammad Yusuf ya shaida wa Blueprint Manhaja ta wayar tarho cewa ‘yan bindigar sun far wa waɗanda lamarin ya rutsa da su ne a lokacin da suke aikin share hanya inda suka kashe takwas daga cikinsu. A cewarsa, an kai harin ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 12:00 na dare. Ya kuma bayyana cewa, a wannan rana mai albarka, an gano gawarwaki uku tare da binne su kamar yadda haƙƙin addinin Musulunci ya…
Read More