Editor

9513 Posts
Cin zarafin yara: Kotu ta tsare wata lauya a Anambra

Cin zarafin yara: Kotu ta tsare wata lauya a Anambra

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kotun hukunta laifukan yara da jima'i da kuma cin zarafin mata ta kai ƙarar wata lauya mai suna Adachukwu Okafor zuwa Sashen Kula da Masu Aikata Manyan Laifuka na jihar (SCID) da ke zama a babban kotun majistare da ke Awka a jihar Anambra. An tsare wacce ake zargin ne a gidan yari bisa zargin yi wa mai aikinta mai shekaru 11 rauni a Onitsha. Wacce ake zargin, mazaunin unguwar Chris Igwilo Street Akapka GRA, 3-3 Onitsha, an gurfanar da ita a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume biyu na aikata laifin da ta yi da…
Read More
An samu ƙaracin ruwan sha a Gusau Babban Birnin Jihar Zamfara

An samu ƙaracin ruwan sha a Gusau Babban Birnin Jihar Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Al'ummar garin Gusau, Babban Birnin Jihar Zamfara na ci gaba da afkawa cikin yanayin matsalar ruwa sha tsawon makonni uku da suka gabata. Binciken da wakilinmu ya gudanar ya nuna cewa wasu yankuna kamar yankin 'reservation' na gwamnati GRA, Gada Biyu, Birnin Ruwa, Tullukawa, Tudun Wada, Gada Baga, Kan-Wuri da dai sauransu na fama da matsalar ƙarancin ruwan sha ga rashin zubar da ruwan da ruwan jihar ya yi na makonni uku na ƙarshe. Wakilinmu ya gano cewa yanzu haka lita 25 na ruwan da masu sayar da ruwan ke siyar da su kan Naira…
Read More
Lawal ya ziyarci wuraren da ‘yan bindiga suka kai hari a Zurmi da Birnin Mgaji

Lawal ya ziyarci wuraren da ‘yan bindiga suka kai hari a Zurmi da Birnin Mgaji

*Ya sha alwashin kawo ƙarshen matsalar tsaro a Zamfara Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya kai ziyara ƙauyukan da suka fuskanci harin 'yan ta'adda domin ƙarfafa musu gwiwa game da sha'anin tsaro ƙarƙashin gwamnatinsa. A makin davya gabata ne 'yan fashin daji suka kai farmaki Nassarawan Zurmi da ke Zurmi da kuma Nasarawan Godel da ke yankin Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji a jihar. Kakakin Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana a cikin sanarwar da ya fitar cewa, Dauda ya yi ziyarar ne domin nuna goyon baya ga al'ummar hare-haren suka shafa da kuma ta'aziyya ga 'yan uwan…
Read More
Kocin Bayern, Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana

Kocin Bayern, Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Koci Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar Bayern Munich a ƙarshen kakar wasa ta bana. Ɗan shekaru 50 ɗin ya maye gurbin Julian Nagelsmann a watan Maris din 2023, inda ya ƙulla yarjejeniyar har zuwa watan Yunin 2025. Sai dai tsohon kocin Chelsea ɗin zai raba gari da ƙungiyar saboda "sauye-sauyen da Bayern ke yi". Tuchel ya jagoranci Bayern lashe gasar Bundesliga a kakar wasan da ta wuce amma a yanzu Bayer Leverkusen ta basu tazarar maki takwas. Sannan kuma an doke Bayern a wasa uku a jere. Shugaban Bayern, Jan- Christian Dreesen ya ce "duka ɓangarorin…
Read More
Ya kamata hukuma ta kawo ƙarshen masu tallan jabun magungunan kashe ƙwari – A.A Na Mazadu

Ya kamata hukuma ta kawo ƙarshen masu tallan jabun magungunan kashe ƙwari – A.A Na Mazadu

Daga ABDULLAHI SANI DOGUWA ABKANO An sake jaddada buƙatar da ke akwai ga shuwagabannin haɗaɗiyar gamayyar masu sayar da magungunan kashe ciyayin da ke hana amfanin gona sakat da magance yawaitar yaɗuwar ƙwari masu kashe amfani, dake kasuwar Abubakar Rimi, Kano, da su yi wani abu da zai kawo ƙarshen babbar matsalar nan ta sayar da jabun magungunan kashe ƙwari , da lamarin ke neman ɓata wa 'ya'yan ƙungiyar suna. Aminu isyaku A.A na mazadu, ɗan kasuwa dake sayar da magungunan kashe ƙwari da illata amfanin gona a rukunin masu sayar da maganin kashe ƙwari a babbar kasuwar Abubakar Rimi…
Read More
An daka wa tirelolin abinci wawa a Jihar Neja

An daka wa tirelolin abinci wawa a Jihar Neja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rahotanni da ga Jihar Neja na bayyana cewa wasu ɓatagari sun tare tireloli maƙil da kayan abinci a yankin Suleja, lamarin da ya sa sojoji suka yi harbi sama don korar su a jiya Alhamis. Wani ganau, Alhassan Abdullahi, ya shaida wa wakilin Daily Trust cewa ɓatagarin, wanda suka ƙona tayoyi sun tare tirelolin da ke tahowa daga Abuja zuwa Kaduna. Ya ce sun sace buhunan kayan abinci iri-iri, musamman shinkafa kafin sojoji su isa wurin. “Allah Ya sanya sojoji sun isa wurin sannan suka fara harbin bindiga a iska don tsoratar da ɓatagarin.…
Read More
Yadda Sunday Igboho ya sake tako ƙafa Nijeriya bayan shekara uku

Yadda Sunday Igboho ya sake tako ƙafa Nijeriya bayan shekara uku

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fiye da shekaru uku bayan ya tsere daga Nijeriya sakamakon samamen da aka kai masa a gidansa da ke Ibadan a ranar 1 ga Yuli, 2021, mai fafutukar kafa ƙasar Yarabawa, Mista Sunday Adeyemo, wanda aka fi sani da Sunday Igboho, a ranar Laraba ya dawo Nijeriya. Jaridar Blueprint Manhaja ta tattaro cewa, ya taso ne daga ƙasar Jamus, inda ya masu mafaka bayan wata kotu a Benion ta bada belinsa a bara. Adeyemo, wanda ya kasance kan gaba a fafutukar tabbatar da ƙasar Yarabawa a ƙarƙashin inuwar Ilana Omo Oodua, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Banji Akintoye,…
Read More
Ƙuncin Rayuwa: Gwamna Sule ya ƙaddamar da shirin bai wa talakawansa tallafi

Ƙuncin Rayuwa: Gwamna Sule ya ƙaddamar da shirin bai wa talakawansa tallafi

Daga BASHIR ISAH A matsayin mataki na rage wa 'yan jihar Nasarawa ƙuncin ratuwar da ake fuskanta a ƙasa, Gwamnan jihar, Abdullhi Sule, ya ƙaddamar da shirin ba da tallafi na musamma inda aka raba kayan abinci da kuɗi ga waɗanda suka samu cin gajiyar shirin. Sule ya ƙaddamar da shirin a yankin rayawa na Azara da ke Ƙaramar Hukumar Awe a jihar, inda aka fara da buhun shinkafa 1,600 da kuɗi N5000 ga kowannensu. An zaɓo waɗanda suka fara cin gajiyar shirin ne daga sassan yankin da suka haɗa da Akiri, Azara, Ribi da kuma Wuse. An ƙaddamar da…
Read More
Gobe za a yi bikin cika shekaru 38 da kafa makarantar BMC a Kano 

Gobe za a yi bikin cika shekaru 38 da kafa makarantar BMC a Kano 

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano A gobe Asabar ne Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Aikin Jarida ta Ƙasa wato Basic Mass Communication School Old Student Association (BAMCOSA) za ta yi taron cikar makarantar shekara 38 da kafuwa da kuma taron shekara-shekara da zai gudana a makarantar da ke Agency for Mass Education daura da makabartar Ɗandolo da ke G/Dutse, Kano. Taron wanda shi ne karo na farko tun kafuwar makarantar, ana sa ran halartar Mataimakin Gwamnan Kano, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo da Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da Kwamishinan Ilimi Alhaji Haruna Doguwa da kwamishinan yaɗa labarai, Baba Halilu…
Read More
Gwamna Dauda ya yaba wa ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya kan yaƙi da matsalar tsaro a Zamfara

Gwamna Dauda ya yaba wa ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya kan yaƙi da matsalar tsaro a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yaba da ƙoƙarin da Gwamnatin Tarayya ke yi wajen magance matsalar rashin tsaron da ta addabi jihar. Dauda ya yi wannan yabon ne a ranar Juma'a kuma a wajen ƙaddamar da babban masallacin Birnin Magaji wanda Hon. Aminu Sanin Jaji ya gina a garin Birnin Magaji, hedikwatar ƙaramar hukumar Birnin Magaji. Gwamnan ya yi kira ga Majalisar Dokoki ta Ƙasa da ta shiga tsakani kan matsalar rashin tsaro sakamakon ayyukan ‘yan bindiga a jihar. "Ina so in nemi agajin Majalisar Dokoki ta Ƙasa da ta tsoma baki cikin gaggawa…
Read More