24
May
Daga AISHA ASAS Hukumar Kula da Walwalar Maniyyata ta Jihar Kano, ta ce ta soma gudanar da shirin wayar da kan maniyyatan jihar a matsayin wani mataki na shirye-shiryen hajjin bana. Sakataren Hukumar, Alhaji Mohammed Abba Danbatta, ya bayyana wa manema labarai a Kano a cewa, shirin wanda aka ƙaddamar da shi a ranar Asabar da ta gabata zai ci gaba da gudana a cibiyoyin yin rajistar hajjin da ake da su a jihar. Ya ce manufar shirin shi ne wayar da kan maniyyatan jihar da kuma ilmantar da su kan tsare-tsaren hanjjin bana da kuma yadda ya kamata su…
