12
May
Daga Aisha ASAS, Abuja Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa ta Nijeriya, Dr. Abubakar Bukola Saraki ya taya ɗaukacin al’ummar musulmin Nijeriya murnar kammala azumin Ramadana na wannan shekara ta 2021, tare kuma da yi musu barka da sallah. Saraki a wata takardar manema labarai, mai ɗauke da sa hannun shugaban sashen ofishin watsa labaransa, Yusuph Olaniyonu ya shawarci ‘yan Nijeriya da su ci gaba da neman kusanci ga Allah tare da yin addu’ar samuwar mafita ga Nijeriya. Ya ƙara da cewa, watan azumin Ramadana ba kawai ya taƙaita ga kyautata halaye na tsawon kwanaki 30 ba ne, lokaci ne da ya kamata mu…
