Editor

9513 Posts
Gwamnati ta kashe naira tiriliyan 2 wajen sayen abinci a 2020

Gwamnati ta kashe naira tiriliyan 2 wajen sayen abinci a 2020

Daga UMAR M. GOMBE Babban Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Sha’anin Tattalin Arziki, Dakta Doyin Salami ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta kashe kusan Naira Tiriliyan 2 wajen sayen kayayyakin abinci daga kasashen ketare tsawon watanni tara, lokacin da dukkanin iyakokin kan tudu ke rufe. Dakta Salami ya fadi haka ne a yayin da yake gabatar da jawabi a taron masu ruwa da tsaki kan makomar tattalin arzikin kasar nan da ya gudana ta kafar bidiyo a Legas a tsakiyar wannan makon. A cewar Dakta Salami duk da rufe iyakokin kan tudu da Nijeriya ta yi, sai da gwamnati…
Read More
Misalin da Sheikh Ahmad Gumi ya kafa

Misalin da Sheikh Ahmad Gumi ya kafa

Tare da IBRAHIM SHEME Ba kasafai Sheikh Dakta Ahmad Gumi ya kan nasa kwan sa ba tare da zakara ba; manufa, ba ya magana ko aikata wani abu ba tare da kwakkwarar hujja ba. Sau da yawa, kalaman sa ba su yi wasu dadi saboda an saba da son jin magana mai dadi, musamman wajen voye gaskiya tare da zama a kan akasin ta. Dakta Gumi ya sha yin suka kan halin rashin tsaro da ake ciki a kasar nan, musamman a Arewa. Kuma ya sha yin nuni da hanyar da ya kamata a bi domin a bulle zuwa inda…
Read More
Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Daga AISHA ASAS, Abuja Gwamnatin Tarayya ta ce, ana sa ran a soma allurar rigakafin cutar korona ya zuwa karshen Maris ko Afrilun 2021.Ministan Lafiya, Osagie Ehanire ne ya bayyana haka sa'ilin da Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da COVID-19 (PTF) ke gabatar da bayanin ayyukankasa, Litinin da ta gabata a Abuja. Ehanire ya ce, "Adadin maganin da Nijeriya ta yi odar sa ta AVATT na Hukumar Hada Kan Afirka, ya danganci daidai adadin da ake bukata ne don gundun barna." Ya ci gaba da cewa, Nijeriya na yin dukkan maiyiwuwa don tabbatar da an yi wa akalla kashi 70…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta kama hanyar kula da ilimin yara marasa galihu

Gwamnatin Tarayya ta kama hanyar kula da ilimin yara marasa galihu

Daga UMAR M. GOMBE a Abuja Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya wakilta Ma'aikatar Jinkai da Agaji da Kyautata Rayuwa ta Kasa, kan ta kula da shirin gwamnati na kokarin kula da yaran da suka daina tafiya makaranta a fadin kasa. Da yake kaddamar da kwamitin mutum 18 da zai ja ragamar shirin a Talatar da ta gabata, Shugaba Buhari ya bayyana cewa ba daidai ba ne ganin yara suna gararamba a tituna da kasuwanni da sauran wurare, ba tare da suna zuwa makaranta ba. Kwamitin zai yi aikinsa ne karkashin jagorancin Ministar Jinkai da Agaji Hajiya Sadiya Umar Farouq tare…
Read More
Cutar korona: NOA ta bukaci ‘yan Nijeriya su ba da hadin kai game da allurar riga-kafin korona

Cutar korona: NOA ta bukaci ‘yan Nijeriya su ba da hadin kai game da allurar riga-kafin korona

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Wayar da Kan 'Yan Kasa ta yi kira ga 'yan Nijeriya da su daina yarda da ra'ayoyi mara tushe da ake yadawa dangane da allurar riga-kafin cutar korona kan cewa maganin na tattare da wasu illoli.  Babban Daraktan hukumar, Garba Abari ne ya yi wannan kira a lokacin bayanin kore zargin da wasu ke yi cewa ana so a yi amfani da allurar ne wajen takaita yawan al'umma, lamarin da Abari ya ce ba gaskiya ba ne. Yana mai cewa, "Babu wata allurar riga-kafin da za a bari a shigo da ita Nijeriya ko a yi…
Read More
Kotu ta dage shari’ar El-Zakzaky zuwa 8 ga Maris

Kotu ta dage shari’ar El-Zakzaky zuwa 8 ga Maris

Kotu ta dage shri'ar El-Zakzaky zuwa 8 ga watan Maris Daga AISHA ASAS A Talatar da ta gabata babbar Kotun Jihar Kaduna da ke shari'ar jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya Ibrahim El-Zakzaky da matarsa  Zeenat, ta dage ci gaba da shari'ar ya zuwa ranar 8 da 9 ga watan Maris mai zuwa. Kotun ta dage shari'ar ne biyo bayan hukuncin da Alkali Gideon Kurada ya yanke dangane da neman kotu ta ba shi lokaci da lauyan El-Zakzaky Mr Femi Falana ya yi a bisa wakilcin Mr Eddie Inegedu, domin ba shi damar nazarin wani bidiyo da wasu shaidu biyu suka…
Read More
UEFA ta fitar da zakarun ’yan wasa na 2020

UEFA ta fitar da zakarun ’yan wasa na 2020

Hukumar Kwallon Kafa ta Nahiyar Turai (UEFA), ta fitar da jerin ’yan wasan da masoya kwallon kafa suka zaba mata, a matsayin tawagar fitattun ’yan wasan ta na shekarar 2020. UEFA ta bai wa masoya kwallon kafa damar soma kada kuri’un su wajen zaba ma ta tawagar ’yan wasa 11 daga ranar 30 ga watan Nuwamba zuwa 6 ga Janairun da muke ciki, inda ’yan wasan Bayern Munich suka fi na kowace kungiya yawa. Tawagar ta shekarar 2020 ko kakar wasan da ta kare, ta kunshi Manuel Neuer na Bayern Munich a matsayin mai tsaron raga. Masu tsaron baya kuma…
Read More
Sarautar Dan Buran Gobir da aka ba ni gadon gidanmu ce – Aminu Alan Waka

Sarautar Dan Buran Gobir da aka ba ni gadon gidanmu ce – Aminu Alan Waka

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano A farkon shekarar nan ne ta 2021 Sarkin Gobir Alhaji Isah uhammad Bawa ya nada shahararren mawaki Alhaji Dakta Aminu Ladan Abubakar Ala, a matsayin Dan Buran Gobir, wanda aka yi wani kasaitaccen bikin nadin sarautar a can Masarautar ta Gobir, kuma jama’a da dama sun halarci bikin.Bayan kammala shagalin bikin nadin mun tattauna da Aminu Ladan Abubakar Ala, domin jin yadda ya samu sarautar da kuma alakar sa da Masarautar Gobir in da ya fara da bayyana mana cewar: To yadda abin ya samo asali dai shi ne, ina da nasaba da Gobirawa, kuma…
Read More
An yanke wa dan Turkiyya shekaru 1,075 a kurkuku

An yanke wa dan Turkiyya shekaru 1,075 a kurkuku

Daga Umar Mohammed Gombe Wata Kotu a Istanbul na kasar  Turkiyya ta daure shugaban wata kungiyar asiri mai suna Adnan Oktar shekaru sama da 1,000 a bisa samun sa da aikata wasu laifuka 10, a cewar wata majiyar shari’a a kasar. An kama Adnan Oktar mai shekaru 64 ne a shekarar 2018, a wani samame da jami’an tsaron kasar suka kai a daidai lokacin da suke tsaka da miyagun laifuka, inda aka kama da yawa daga mabiyan sa wadanda yawancin su mata ne. Ana tsare da shi tun watan Yunin 2018 a matsayin wani bangare na fatattakar kungiyar sa da…
Read More
Matsalar Tsaro: Makarfi ya gargadi ‘yan Nijeriya

Matsalar Tsaro: Makarfi ya gargadi ‘yan Nijeriya

Daga Aisha Asas Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Sanata Ahmed Mohammed Makarfi, ya ja hankulan 'yan Nijeriya a kan su daina barin son zuciyarsu yana tasiri wajen daukar matakai wanda hakan ka iya haifar da rikici. Makarfi ya nuna bukatar da ke akwai 'yan Nijeriya su fahimci cewa matsalar tsaron da ke addabar kasar nan aba ce da ke bukatar a yi mata taron dangi domin dakile ta. Yana mai cewa, "Wannan matsala ce da ta shafe mu baki daya." Makarfi ya yi wadannan bayanan ne a wata sanarwa da ya fitar inda ya nuna damuwarsa kan tabarbarewar sha'anin tsaron Nijeriya.…
Read More