ukarofi

11668 Posts
Za mu gyara albashin sarakuna da malamai a jihar Bauchi– Gwamna Bala

Za mu gyara albashin sarakuna da malamai a jihar Bauchi– Gwamna Bala

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad ya shaida wa BBC cewa lambar yabon da wata gidauniya da haɗin gwiwar gwamnatin Nijeriya suka karramashi da ita, babbar nasara ce.Sanata Bala ya ce an ba shi lambar yabo ta ayyukan birane, sakamakon irin ayyukan da gwamnatinsa ke yi a jihar Bauchi, ya kuma ce a yanzu zai mayar da hankali kan ƙara inganta tsaro a jiharsa.''Tsaro na ɗaya daga cikin abin da zai kawo huɓɓasa wajen ci gaban garuruwa da biranen da ƙauyukanmu, idan ƙauyuka ba su zauna lafiya ba, to kuwa birane ba za su…
Read More
Biyan ‘yan kwangila akan lokaci yana bunƙasa tattalin arzikin jihar Kano – Engr. Khalil

Biyan ‘yan kwangila akan lokaci yana bunƙasa tattalin arzikin jihar Kano – Engr. Khalil

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano An yi amanna cewa biyan ƴan kwangila akan lokaci yana inganta tattalin arzikin jihar Kano. Manajan Daraktan Kamfanin Gerawa Global, Engr. Abubakar Ibrahim Khalil ne ya bayyana hakan a lokacin da gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya kaddamar da titin kilomita biyar da aka gina a Gwarzo, wanda gwamnatin baya ta yi watsi da shi. Engr Abubakar Khalil ya kara da cewa, bayar da kwangiloli ga kamfanoni na cikin gida na rage rashin aikin yi a tsakanin matasan Kano da sauran al'umma, Kazalika ya yabawa Gwamnan Jihar Kano bisa yadda ya ke baiwa…
Read More
‘Yan Boko Haram 69 sun miƙa wuya ga rundunar MNJTF

‘Yan Boko Haram 69 sun miƙa wuya ga rundunar MNJTF

Daga SANI AHMAD GIWA a AbujaMayaƙan ƙungiyar Boko Haram 69 da ‘yan uwansu sun miƙa wuya ga Rundunar Haɗin Gwiwa ta Ƙasa da Ƙasa (MNJTF) a Kamaru da Nijar da ke yankin Tafkin Chadi.Babban jami’in yaɗa labarai na rundunar soji da ke N’djamena-Chad, Laftanar-Kanar Abdullahi Abubakar a wata sanarwa ya ce, ’yan tayar da ƙayar bayan sun miƙa wuya ne a tsakanin ranakun 1 zuwa 6 ga watan Yulin 2024, yayin da rundunar Operation Lake Sanity 2 ke ci gaba da samun nasara a kansu.Laftanar-Kanar Abubakar ya bayyana cewa, farmakin da sojojin Kamaru da Nijeriya ke kaiwa a Tafkin Chadi,…
Read More
Babu auren jinsi a ‘Yarjejeniar Samoa’ — Ƙungiyar Lauyoyi

Babu auren jinsi a ‘Yarjejeniar Samoa’ — Ƙungiyar Lauyoyi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta ce 'Yarjejeniyar Samoa' da gwamnatin ƙasar ta sa hannu a kai ba ta da wata alaƙa da auren jinsi da ake cece-kuce a kai.Shugaban NBA, Yakubu Maikyau, ya ce ƙungiyar na da hannu wajen sanya hannu kan yarjejeniyar Samoa kuma babu wani ɓangare na yarjejeniyar da ke da alaƙa da ’yan luwaɗi da maɗigo, ko auren jinsi (LGBTƘ).Shugaban na NBA ya ce ƙungiyar ta lura da ce-ce-ku-cen da ake a Nijeriya kan rattaɓa hannu da ƙasar ta yi kan yarjejeniyar Samoa wanda ake zargin an sharɗanta mata amincewa da…
Read More
Yunƙurin kashe kai: An tura Shu’aibu Yashau wurin auna lafiyar ƙwaƙwalwa

Yunƙurin kashe kai: An tura Shu’aibu Yashau wurin auna lafiyar ƙwaƙwalwa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar ’yan sandan Babban Birnin Tarayya, Abuja ta aike da mutumin da aka kama da yunƙurin kashe kansa zuwa Cibiyar Kula da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa (SDS) domin tantance lafiyar ƙwaƙwalwasa.Idan ba a manta ba, a ranar Litinin ne ‘yan sanda suka kama Shu’aibu Yushau da laifin hawa tsaunin gidan rediyon ASO da ke Katampe, Abuja, da yunƙurin kashe kansa.Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan babban birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya cewa, za a ɗauki mataki kan wanda ake zargin idan…
Read More
Dogarin Tinubu ya zama sabon Sarkin Ilemona a Jihar Kwara

Dogarin Tinubu ya zama sabon Sarkin Ilemona a Jihar Kwara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An naɗa Laftanar Kanal Nurudeen Yusuf, dogarin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a matsayin sabon Sarkin Garin Ilemona da ke Jihar Kwara.Rahotanni sun bayyana cewa a halin yanzu Yusuf na kan karagar mulki ne a matsayin 'Adele' (Shugaba) domin duba al’amuran garin har sai ya yi ritaya daga aikin Soja.Yusuf dai ɗa ne ga marigayi sarki Oba Yusuf Omokanye Oyekanmi, Elemona na Ilemona a ƙaramar hukumar Oyun a Jihar Kwara.Bayan ya kammala karatunsa na digiri a fannin kimiyyar na'ura mai kwakwalwa daga kwalejin fasaha ta Offa a shekarar 2000, Yusuf ya shiga makarantar horar da sojoji ta…
Read More
A Nijeriya an samu kisan kai guda 1,702 a 2023

A Nijeriya an samu kisan kai guda 1,702 a 2023

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ta bayyana cewa, an samu kashe-kashen kai har guda 1,702, garkuwa da mutane 2,149 da kuma laifuka 320 na fashi da makami a faɗin ƙasar a shekarar 2023.A wani rahoto da ƙungiyar ƙididdigar tattara bayanai ta fitar a ranar Juma’a 5 ga Yuli, 2024, ya nuna cewa yankin Arewa ta Tsakiya ne ya fi kowacce yawan al’amuran kisan kai, wanda ya kai 436 a shekara.A cikin shekarar da ta gabata, yankin Arewa maso Yamma ya samu laifukan kisan kai 417, yankin Arewa maso Gabas yana da 345, sannan Kudu maso Yamma ya…
Read More
Rikicin Masarautar Kano: APC ta sha alwashin koya wa NNPP darasi a 2027

Rikicin Masarautar Kano: APC ta sha alwashin koya wa NNPP darasi a 2027

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jam’iyyar APC ta tabbatar da cewa jam’iyyar NNPP za ta faɗi warwas a zaɓen 2027 saboda matsayar da ta ɗauka kan rikicin masarautar Kano.A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja, shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Abdullahi Abbas, ya bayar da hujjar cewa lamarin zai yi mummunar tasiri ga damar zaɓen NNPP, wanda hakan zai bai wa Shugaba Bola Tinubu nasara.Ya yi iƙirarin cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ba shi da wani shiri na zama shugaban Nijeriya.A cewar Abbas, jam’iyyar APC a yanzu ta samu haɗin…
Read More
An kuɓutar da limamin coci bayan sati biyu da sace shi a Zamfara

An kuɓutar da limamin coci bayan sati biyu da sace shi a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An sako Fafa Mikah Suleiman, Babban Limamin Cocin Katolika na St. Raymond da ke Damba, Gusau a Jihar Zamfara, bayan da wasu ’yan bindiga suka yi garkuwa da shi tsawon makonni biyu.An tabbatar da sakin sa ne a ranar Lahadi, 7 ga Yuli, 2024, a cikin wata sanarwa da Pascal Salifu, Daraktan Sadarwa na Diocese na Katolika a Sokoto ya fitar.“Mun yi matuƙar farin cikin sanar da sakin Fr Mikah Suleiman, wanda aka yi garkuwa da shi ranar 22 ga watan Yuni, 2024,” inji sanarwar.“Mu na miƙa godiyar mu ga Allah da ya kiyaye shi da…
Read More
NNPP ta zargi Tinubu da goyon bayan Aminu Ado Bayero

NNPP ta zargi Tinubu da goyon bayan Aminu Ado Bayero

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Jam'iyyar NNPP mai mulki a Jihar Kano, Dr Hashimu Dungurawa ya zargi shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da hannu a hana ruwa gudu a rikicin masarautar Kano da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa tsakanin Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero.Da yake zantawa da manema labarai a ranar Lahadin da ta gabata game da nasarorin da jam’iyyar NNPP ta samu a cikin shekarar da ta gabata, Dungurawa ya bayyana cewa hakan hujja ce kan yadda aka turo sojojin Nijeriya, ’yan sanda, DSS, da sauran jami’an tsaro domin su bai wa Sarki Bayero kariya ta…
Read More