Kasuwanci

Ƙarancin dakon man fetur ne ya haifar da wahalarsa a ƙasa – IPMAN

Ƙarancin dakon man fetur ne ya haifar da wahalarsa a ƙasa – IPMAN

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ƙungiyar Dillalan Man Fetur Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, IPMAN, ta ɗora alhakin ƙarancin dakon man fetur da ake samu daga defo na Legas a dalilin da ya haifar da wahalar man da ake fuskanta a Abuja da sauran sassan ƙasar. Shugaban ƙungiyar ta IPMAN, Chinedu Okoronkwo ne ya bayyana haka a wata hira da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN ranar Litinin a Legas. Okoronkwo ya yi magana kan yadda layukan mai ke sake dawowa a wasu sassan ƙasar nan, musamman a Abuja. Ya ce yaƙin Rasha da Ukraine ya kawo cikas ga…
Read More
Kotu ta umarci kamfanin MTN su biya diyyar miliyan 200 ga yarinya ‘yar shekara 4

Kotu ta umarci kamfanin MTN su biya diyyar miliyan 200 ga yarinya ‘yar shekara 4

Daga AMINA YUSUF ALI Wata kotun dake zamanta a garin Damaturu ta jihar Yobe a ranar Litinin ɗin da ta gabata ta umarci hukumar kamfanin sadarwa na MTN (NELMACO) da su biya Hamsatu Abdullahi Naira miliyan 200 saboda sakaci. Ita dai wanna yarinya mai suna Hamsatu ana zargin cewa, ta rasa hannayenta guda biyu da kuma ƙafa guda a sakamakon shokin ɗin wutar lantarki daga wayoyin kamfanin MTN. Alƙalin kotun Mai Shari'a M. Lawu Lawan ya bayyana cewa, waɗanda ake zargin, wato (MTN) sun riga sun amsa laifinsu a baki da kuma a rubuce kasancewar akwai shaidu masu ƙarfi da…
Read More
Yadda wata babbar dillaliyar miyagun ƙwayoyi a Delta ta shiga hannu

Yadda wata babbar dillaliyar miyagun ƙwayoyi a Delta ta shiga hannu

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) ta yi nasarar cafke wata mata mai shekaru 59, wadda aka tabbatar ita ce shugabar dillalan muggan ƙwayoyi a Jihar Delta da maƙwabtanta. Premium Times ta rawaito cewa: Matar mai suna Bridget Emeka, an fi sanin ta da suna Mama. An kama ta ne a ranar Lahadi, a wani danƙareren gidanta da ke garin Warri a jihar Delta. Kakakin yaɗa labaran NDLEA, Femi Babafemi ne ya sanar da haka a ranar Talata a Abuja. NDELA sun zargi Mama da riƙa yin amfani da kantamemen gidanta dake kan Titin…
Read More
Yadda tsananta haraji ga kamfanonin sadarwa ya jawo matsalar sabis ɗin layukan waya a Nijeriya

Yadda tsananta haraji ga kamfanonin sadarwa ya jawo matsalar sabis ɗin layukan waya a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotanni sun nuna cewa, tsananin yawan harajin da gwamnatin Nijeriya take tafka wa kamfanonin sadarwa shi ne ummul'aba'isin na rashin ƙarfin sabis ɗin layukan waya a ƙasar nan.  Wannan rahoto yana ƙunshe ne a wani rahoto da  SB Morgen suka  haɗa.  Rahoton ya bayyana cewa, kamfanonin sadarwar suna azabtuwa daga haraji da ya zarta ƙa'ida da gwamnatin Nijeriya take ta lafta musu. Rahoton ya bayyana cewa, a yanzu haka akwai haraji iri daban-daban har kala 40 wanda kamfanonin sadarwa suke biya a Nijeriya. Sai dai inda matsalar take a cewar rahoton, wannnan gingimemen haraji shi ya…
Read More
Ya kamata a sanya biyan haraji a cikin sharauɗɗan tantance ‘yan takara a Nijeriya – FIRS

Ya kamata a sanya biyan haraji a cikin sharauɗɗan tantance ‘yan takara a Nijeriya – FIRS

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar tattara haraji ta tarayyar ƙasar nan (FIRS) ta matsa lamba a kan gwamnati ta sanya biyayya wajen biyan haraji a matsayin ɗaya daga cikin sharauɗɗan tantance kowanne mai sha'awar takarar kujerun muƙamin gwamnatin ƙasar nan. Shugaban hukumar ta  FIRS, Muhammad Nami shi ya bayyana wannan buƙata tasa a wata ganawa da suka yi da hukumar zaɓe ta Nijeriya (INEC) a ranar Talatar da ta gabata a Abuja. Taron ganawar an yi shi ne don samun haɗin gwiwa da fahimtar juna a tsakanin wasu hukumomin tarayyar ƙasar nan. Hakazalika, hukuma mai zaman kanta ta yaƙi da…
Read More
MTN ya yi asarar Naira biliyan 427.44, Airtel ya zama babban kamfanin Nijeriya

MTN ya yi asarar Naira biliyan 427.44, Airtel ya zama babban kamfanin Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai kamfanin sadarwa na MTN ya samu faɗuwar wuri na gugar wuri har Naira biliyan 427.44. wannan ya ba wa abokin burminsa kamfanin Airtel dama ya zarce shi zuwa matsayin ma fi girman kamfanin a Nijeriya.  Masu sharhi a kan al'amarin sun bayyana cewa, abin da matuƙar mamaki. Domin a ranar Alhamis ɗin makon da ya gabata ne dai MTN ƙarfin hannun jarinsa ya yi tashin da bai taɓa yi ba a cikin makwanni 52. Wato inda ya kai kusan Naira tiriliyan shida.  Amma sai dai hauhawar ribar ba ta yi tsawon rai…
Read More
Ɗangote na neman rancen Naira biliyan 638 kafin 2023

Ɗangote na neman rancen Naira biliyan 638 kafin 2023

Daga AMINA YUSUF ALI Mutumin da ya fi kowa arziki a Afirka, Alhaji Aliko Ɗangote yana buƙatar rancen Naira biliyan 638 don ƙarasa ginin matatar man wacce yake so ya kammala kafin nan kafin shekarar 2023. Kamar yadda jaridar Ingilishi ta News Business News ta rawaito.  A wani sakamakon rahoto da kamfanin Fitch wanda ya yi fice wajen bincike a Duniya ya yi hasashen cewa, mutumin da ya fi kowa kuɗi a Afirka, Ɗangote dole zai buƙaci rancen Naira biliyan 638 don kammala matatar man da ya fara ginawa wacce ake sa ran za ta lamushe har Dalar Amurka biliyan…
Read More
’Yan Nijeriya na shanye barasa da lemon kwalba na Naira biliyan 246 a wata uku – Rahoto

’Yan Nijeriya na shanye barasa da lemon kwalba na Naira biliyan 246 a wata uku – Rahoto

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotanni sun bayyana cewa, a cikin kowanne watanni uku 'yan Nijeriya sukan kwankwaɗe barasa da lemunan kwalaba na wuri na gugar wuri har na sama da biliyan Naira 245.61. Sakamakon wani rahoto mai taken Q1 2022 da aka gudanar a kan manyan rukunin kamfanonin samar da ababen sha guda uku wato, kamfanonin gida Nijeriya, kamfanonin wajen ƙasar nan da kuma kamfanin Guinness Nigeria ya bayyana cewa, yadda yawan masu yi wa kamfanonin ciniki yake ƙaruwa ya tilasta kamfanonin ƙara zagewa wajen ganin ababen shan ba su yanke wa masu saye ba.  Wannan ba makawa shi ya…
Read More
Abinda ke jawo yawaitar ficewar kamfanonin mai na ƙasar waje daga Nijeriya (2) – Sani Ɓaɓura

Abinda ke jawo yawaitar ficewar kamfanonin mai na ƙasar waje daga Nijeriya (2) – Sani Ɓaɓura

Daga AMINA YUSUF ALI Komai na tafiya daidai wajen haqo mai a Nijeriya har wajen ƙarshan 1980 zuwa farkon 1990 lokachin da guraren haƙar man suka fara fuskantar matsaloli kamar haka: Guraren ƙauyuka ne futuk, babu ruwan sha mai tsafta, ba wutar lantarki, gidajensu na bukka ne a kan ruwa suke kwana, suke bahaya, makarantun 'ya'yansu ginin ƙasa ne, rufin ciyayi; kuma duk lokacin da bututun dake ɗauke da mai ya fashe, sana'arsu ta kamun kifi da noma ta  shiga uku. Hakazalika, sai sun yi tafiya a kwale-kwale mai nisa kafin su sami ruwan da za su sha. Ƙauyukan kuwa…
Read More
Jamhuriyar Afirka ta tsakiya (CAR) ta mayar da Bitkoyin kuɗin ƙasarta

Jamhuriyar Afirka ta tsakiya (CAR) ta mayar da Bitkoyin kuɗin ƙasarta

Daga AMINA YUSUF ALI Jamhuriyar mulki ta Afirka ta tsakiya (CAR) ita ma ta bi sahun El Salvador wajen mayar da Bitkoyin a matsayin kuɗinta na ƙasa. Jaridar Sierra Leone Telegraph ta bayyana cewa, Afirka ta Tsakiya wacce a kwanakin baya yaƙi ya yi wa raga-raga da ita, ta ƙaddamar da Bitkoyin a matsayin kuɗin ƙasarta na halaliya wanda za a iya yin dukkan wata hada-hadar ta kuɗi, kamar cinikayya, ko harkar banki da sauransu. Sai dai wannan mataki da ƙasar ta ɗauka ya jawo mata cece-ku ce, domin ana zargin ƙasar ta yi gaban kanta ne ba tare da…
Read More