Kasuwanci

Raha nake yi, cewar matar da ta ce ta tara Naira biliyan guda da cinikoin ƙuli-ƙuli

Raha nake yi, cewar matar da ta ce ta tara Naira biliyan guda da cinikoin ƙuli-ƙuli

Daga AMINA YUSUF ALI Wata matashiyar mai suna Angela Job Emodiae, wacce ta yi ikirarin cewa ta haɗa Naira biliyan guda a cinikin ƙuli-ƙuli, ta yi amanta ta lashe. Inda ta bayyana cewa ta faɗa ne kawai don saboda raha.   Idan za a iya tunawa, a ranar Asabar ɗin da ta gabata ne, 7 ga watan Janairun 2023 matashiyar mai suna Angela wacce take zaune a garin Jos ta jihar Filato, mamallakiyar kamfanin Anjees Food, ta wallafa a shafinta na dandalin Fesbuk cewa, ta haɗa Naira biliyan guda a kan cinikin ƙuli-ƙuli. Sannan ta ƙara da cewa, a wannan shekara…
Read More
Sababbin takardun kuɗi: Majalisar dattijai ta nemi CBN ya ɗage wa’adin daina amsar tsofaffin kuɗi

Sababbin takardun kuɗi: Majalisar dattijai ta nemi CBN ya ɗage wa’adin daina amsar tsofaffin kuɗi

Daga AMINA YUSUF ALI Majalisar dattijai ta Nijeriya ta yi kira ga Babban Bankin Nijeriya (CBN), da ya ƙara wa'adin daina amfani da tsofaffin takardun Naira daga 31 ga watan Janairun 2023 da ya sa, ya mayar zuwa 30 ga watan Yunin 2023. Idan ba a manta ba, a watan da ya gabata ne, wato a ƙarshen shekarar bara ta 2022 ne dai CBN ya gabatar da sababbin takardun kuɗin da aka sauya fasalin su, wato Naira 1,000, da Naira 500 da kuma Naira 200 da ya yi wa canjin fuska, tare da ba da sanarwar cewa, sababbin takardun za…
Read More
Sabuwar dokar haraji: Daraktocin kamfanonin sufurin jirgin sama za su iya fuskantar ɗaurin shekaru 2 a gidan yari

Sabuwar dokar haraji: Daraktocin kamfanonin sufurin jirgin sama za su iya fuskantar ɗaurin shekaru 2 a gidan yari

Daga AMINA YUSUF ALI Masu tafiyar da harkar sufurin jiragen sama a Nijeriya suna fuskantar barazanar ɗaurin shekaru biyu a kurkuku ko zaɓin biyan tarar Naira miliyan biyar ko dukkan biyun a sakamakon qin biyan haƙƙin gwamnati da ta sanya dokar kamfanonin su dinga biyan kaso 5% na kowanne kuɗin tikiti da aka saya na jirgi ko kuma idan aka biya kuɗin jirgin ɗaukar kaya da sauran kwangiloli. Hukumar kula da harkar sufurin jirgin sama ta Nijeriya (NCAA) ita ta bayyana haka a ranar Talatar Makon da ya gabata. Inda ta gabatar da wannan sabuwar doka da take son tabbatarwa…
Read More
NERC ta yi ƙarin kuɗin wuta a ɓoye

NERC ta yi ƙarin kuɗin wuta a ɓoye

Daga WAKILINMU Hukumar Kula da Rarraba Wutar Lantarki ta Nijeriya (NERC), ta ƙara kuɗin wutar lantarki a ɓoye ba tare da sanin 'yan ƙasa ba. NERC ta yi haka ne ta hanyar bai wa kamfanonin rarraba lantarki umarnin su ƙara kuɗun wutar da suke bai wa jama'a. Kamfanin Rarraba Lantarki na Abuja (AEDC), ya tabbatar da ƙarin farashin a saƙonsa da ya wallafa a shafinsa na Tiwita ranar Laraba. Saƙon ya ce, “Barka dai, a sani cewa ƙarin farashin lantarki umarni ne daga NERC.” Ya zuwa haɗa wannan labari, babu wani bayani a hukumance daga daga NERC kan batun.
Read More
Gurɓatar yanayi: Kamfanin Shell ya amince da biyan diyyar Yuro miliyan 15 ga manoman Nijeriya

Gurɓatar yanayi: Kamfanin Shell ya amince da biyan diyyar Yuro miliyan 15 ga manoman Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Bayan doguwar Shari'a da aka shafe tsahon shekaru ana yi, Kamfanin tace man fetur na ƙasar waje, Shell ya amince da biyan diyyar wuri na gugar wuri har Yuro miliyan 15 ga wasu manoman Kudancin Nijeriya guda 3 da ƙauyukansu a yankin Neja Delta. Kotun mai zamanta a ƙasar Holan ita ta yanke wannan hukunci tun a shekarar 2021. Inda ta umarci kamfanin da ya biya diyyar garin man fetur da ya faru ta sanadiyyar kamfanin Shell a wasu ƙauyuka a Neja Delta a tsakanin shekarar 2004 da 2007. Rahotanni sun bayyana cewa, tun a wancan…
Read More
Jiragen ruwa maƙare da man fetur sun maƙale a kan teku ana tsaka da ƙarancin mai a Nijeriya

Jiragen ruwa maƙare da man fetur sun maƙale a kan teku ana tsaka da ƙarancin mai a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI A yayin da ake tsaka da ƙaranci da tsadar man fetur da ya ƙi ci, ya qi cinyewa a Nijeriya, a yanzu haka jiragen ruwa waɗanda suke maqare da man fetur, gas, baƙin mai da man jirgin sama suna nan suna jiran sahalewar dakarun tashar jirgin ruwan Legas don sauke kayansu. Duk kuwa da tsada da ƙarancin man fetur da ake ciki a ƙasar da ta kai ga ana sayar da man fetur daga Naira 170 yanzu ya koma 260 kowacce lita a gidajen mai, wasu gidajen ma an garwaye su saboda babu ma man da…
Read More
Kudancin Nijeriya ya ba wa Arewa tazarar shekaru 40 a fuskar arziki – Bankin Duniya

Kudancin Nijeriya ya ba wa Arewa tazarar shekaru 40 a fuskar arziki – Bankin Duniya

AMINA YUSUF ALI Bankin Duniya ya bayyana cewa, jihohin Arewacin Nijeriya sai sun ɗauki tsahon shekaru 40 kafin su kamo jihohin Kudu a fannin tattalin arziki duba da yanayin yadda abubuwa suke tafiya a halin yanzu. Bankin ya bayyana cewa, yanayin rashin cigaba da bunƙasa da yankin Arewa yake yi na tsahon lokaci shi ya jawo wannan wawakekiyar tazara a tsakanin yankunan guda biyu. A cewar Bankin an bar yankin Arewa a baya a fannoni kamar noman zamani, harkar ma'adanai da masana'antu. Wannan ra'ayi yana ƙunshe ne a wani jawabi a kan tattalin arzikin Nijeriya (CEM) wanda bankin ya saki…
Read More
CBN ya taƙaita cire kuɗi a POS zuwa dubu N20 a rana ɗaya

CBN ya taƙaita cire kuɗi a POS zuwa dubu N20 a rana ɗaya

*Ya fitar da sabbin dokokin hada-hadar kuɗi Daga WAKILINMU Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya taƙaita yawan kuɗin da mutum zai iya cirewa a na’urar POS a rana ɗaya zuwa N20,000, a banki kuma ba za su wuce N100,000 ba a mako guda. Hakan na ɗaya daga cikin irin matakan da babban bankin ya ce zai fito da su domin taƙaita yawon tsabar kuɗi a hannun mutane. Ana sa ran wannan tsari ya soma aiki ya zuwa ranar tara ga watan Janairu, 2023. Wannan na zuwa ne a lokacin da CBN ke shirye-shirye sakin sabbin takardun Naira da aka sake wa…
Read More
Tun zamanin Jonathan rabon da NNPC ya sanya ko ƙwandala a asusun CBN – Emefiele

Tun zamanin Jonathan rabon da NNPC ya sanya ko ƙwandala a asusun CBN – Emefiele

Daga AMINA YUSUF ALI Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya koka da yadda NNPC ya daina turo da Daloli kowanne wata ga asusun CBN ɗin. Wato wanda ya saba turowa na cinikin man fetur na ƙasashen waje zuwa ga CBN a kowanne wata. A cewar Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, rabon da CBN ya ga wannan kuɗin na wata-wata da aka saba sakawa a asusunsa tun lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan. Wato tun daga shekarar 2014 kenan. Gwamnan Babban Bankin Nijeriya CBN, Mista Godwin Emefiele ya bayyana takaicinsa a kan yadda kamfanin samar da man fetur ya daina zuba kuɗaɗen…
Read More
Yadda bankunan Nijeriya ba sa iya taɓuka komai yayin da kuɗin masu ajiya suka yi ɓatan dabo

Yadda bankunan Nijeriya ba sa iya taɓuka komai yayin da kuɗin masu ajiya suka yi ɓatan dabo

Daga AMINA YUSUF ALI "Abin ya sha kanmu, je ki CBN ki kai kukanki!" Wannan ita ce amsar da mahukuntan wani banki suka ba wa wata mata bayan da kuɗaɗenta har Naira 91,900 suka ɓace ɓat, daga asusun ajiyarta na bankin. Ita dai wannan mata mai suna Rebecca Jolaoso, 'yar kasuwa ce 'yar asalin garin Ibadan. Rebecca ta zayyyana yadda Bankin Polaris ya kasa yi mata wani kataɓus bayan Naira 91,900 zuwet ta fita daga asusun ajiyarta na bankin Polaris ba bisa ƙa'ida ba. Duk kuwa tana tare da katin cirar kuɗinta a tare da ita. Rebecca ta bayyana cewa,…
Read More