Kasuwanci

Nijeriya za ta soma fitar da shinkafa zuwa Masar duk da ƙarancin abincin da yake damun ƙasar

Nijeriya za ta soma fitar da shinkafa zuwa Masar duk da ƙarancin abincin da yake damun ƙasar

Daga AMINA YUSUF ALI A yayin da ƙasar Nijeriya take fama da matsanancin ƙaranci da tsadar kayan abinci kama daga hatsi har kayan masarufi, musamman shinkafa wacce aka fi amfani da ita a kodayaushe. A yanzu haka ƙasar ta ƙulla wata yarjejeniya da ƙasar Masar don ta dinga kai musu shinkafa. A yanzu haka dai ƙungiya mai zaman kanta ta manonman shinkafa a Nijeriya (RIFAN) da wani kamfani mai zaman kansa a Nijeriya sun rattaba hannaye a wata yarjejeniyar fahimtar juna tsakaninsu da ƙasar ta Misira don a fara sayar musu da shinkafar da aka noma a gida Nijeriya. Wannan…
Read More
Nijeriya tana fuskantar mafi munin matsin tattalin arziki a tarihi – Rahoton bincike

Nijeriya tana fuskantar mafi munin matsin tattalin arziki a tarihi – Rahoton bincike

Daga AMINA YUSUF ALI A cikin watan Oktoba na bana dai matsin tattalin arzikin Nijeriya ya sake ƙaruwa da kaso 21.09. Waɗannan alƙalumman sun kasance mafi munin halin matsin tattalin arzikin da ƙasar ta taɓa shiga a tarihi. Wannan bayani dai ya samu ne daga sakamakon binciken ƙididdigar farashi ta (CPI) da hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) suka yi a cikin watan Oktoban 2022. CPI ta auna kimar canjin kuɗaɗe a kan farashin kaya da ayyuka, inda ta gano sun yi gudun wuce sa'a har i zuwa ƙarin kaso 21.09 saɓanin yadda yake a kaso 20.77 a watan Satumban bana.…
Read More
Nahiyar Turai ta soma gangamin zawarcin ƙarfafa alaƙar kasuwanci da Nijeriya

Nahiyar Turai ta soma gangamin zawarcin ƙarfafa alaƙar kasuwanci da Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI Gamayyar ƙasashen Turai (EU), ta fara zawarcin son ƙara ƙarfafa alaƙar ciniki ta da Nijeriya. Wannan shiri shi ne mafi girman shirin da EU ta fara yi a wajen iyakokinta. Wato shirin nan mai taken 'Mun ga Afirka' ya fara tafiya ba tangarɗa a ƙasashen Nijeriya Kamaru, Kongo, Tanzania da Zimbabwe, kuma ana sa ran zai bi sahun sauran ƙasashen Afirka guda 7 da aka fara gudanar da shi a baya, a tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021. Shirin yana harin matasan Nijeriya masu shekaru kamar 18 zuwa 35 waɗanda suke da ido a harkar fasahar zamani.…
Read More
Har a Amurka ana sana’ar sayar da kayan Gwanjo – Bashir (Chef BNG)

Har a Amurka ana sana’ar sayar da kayan Gwanjo – Bashir (Chef BNG)

Daga AMINA YUSUF ALI Wani Bahaushe ɗan asalin jihar Kano mazaunin garin Maryland dake ƙasar Amurka, Bashir Ibrahim Na'iya ya ziyarci shafinmu mu na kasuwanci a wannan mako, inda ya bayyana asalin sirrin yadda sana'ar Gwanjo take. A sha karatu lafiya. Asalin kayan gwanjo da inda ake samun su har ya zama sana'a. Da farko zan fara da magana a kan rubutuna na farko wanda wasu suka ɗauka kayan gwanjo a bola ko shara ake samo su, sam ba haka ba ne. ba haka, Kawai dai na san na taɓa ganin waɗannan kayan a bola ya tuno min da wani…
Read More
FIRS ta fara amsar haraji kai-tsaye daga masu manhajojin wasanni na yanar gizo

FIRS ta fara amsar haraji kai-tsaye daga masu manhajojin wasanni na yanar gizo

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar tattara haraji ta birnin Tarayyar (FIRS) ta fara cirar haraji daga manhajojin wasannin na yanar gizo ta hanyar zarar harajin a duk yayin da suka yi hada-hadar kuɗi. A wata sanarwar da shugaban zartarwar hukumar, Mista Muhammad Nami ya sanya wa hannu, an bayyana cewa, wannan hukunci na fara zarar harajinta ya samu goyon bayan dukkan mamallakan manhajojin wasannin na yanar gizo. Shi dai wannan tsari na cire harajin nan take wani tsarin cire haraji nan take ne a duk lokacin da manhajojin wasannin suka yi hada-hadar kuɗin ta banki. Sannan kuma a take a…
Read More
Sauya fasalin Naira ba zai magance matsin tattalin arziki a Nijeriya ba -Moghalu

Sauya fasalin Naira ba zai magance matsin tattalin arziki a Nijeriya ba -Moghalu

Daga AMINA YUSUF ALI Tsohon Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, (CBN), Kingsley Moghalu ya yaba da matakin Gwamnatin Tarayya na sauya fasalin Naira amma sai da ya yi gargaɗin cewa, sauya fasalin kuɗin ba hanya ce da za ta ceto ƙasar daga matsin tattalin arzikin da take ciki ba. A makon da ya gabata ne dai CBN ya ba da sanarwar sauya fasalin takardun Naira 200, 500 da kuma 1000, inda ta bayyana cewa, sabon kuɗin zai fara aiki ne daga tsakiyar watan Disambar shekara ta 2022 da muke ciki. Kodayake, al'amarin ya jawo cece-ku-ce da muhawara mai zafi tsakanin…
Read More
ATSSSANA ta dakatar da aiki a Filin Jirgin Saman Murtala saboda korar mabobinta daga aiki

ATSSSANA ta dakatar da aiki a Filin Jirgin Saman Murtala saboda korar mabobinta daga aiki

Daga BASHIR ISAH A ranar Talata ma'aikatan Babban Filin Jirgin Saman Murtala Mohammed da ke Legas suka yi zanga-zanga tare da rufe ƙofar shiga filindomin nuna rashin jin daɗinsu dangane da korar wasu jagororinsu da aka yi daga aiki. Wannan al'amari ya jefa matafiya da suka kasance a filin jirgin a wannan lokaci cikin mawuyacin hali kasancewar masu zanga-zangar sun dakatar da komai a filin jirgin. Jiragen da suka kasa samun sararin tashi a wannan lokaci sun haɗa da Ibom Air da Air Peace. Sanarwar da ƙungiyar ma'aikatan (ATSSSAN) ta fitar, ta nuna kora daga aikin ta shafi wasu jagororin…
Read More
Yadda matatar Fatakwal ta lamushe biliyan N39.4 a shekara ba tare da taɓuka komai ba

Yadda matatar Fatakwal ta lamushe biliyan N39.4 a shekara ba tare da taɓuka komai ba

Daga AMINA YUSUF ALI Duk da rashin tavuka komai a fannin tattalin arzikin ƙasa da matatar man fetur ɗin Nijeriya dake a garin Fatakwal take yi, a cikin watanni 12 kacal ta lamushe kuɗaɗen da yawansu ya kai Naira biliyan 39.4. Wannan matatar dai an ruwaito ta lamushe Naira 39,491,468,000 a cikin shekarar 2021 duk kuwa da ta kwashe shekaru ba tare da tace ko da ɗigon man fetur guda ba. Waɗannan bayanan sun zo ne daga rahotannin bayanan kuɗin na Kamfanin Samar da Man Fetur na Nijeriya (NNPCL) wanda hukumar PHRC ta gudanar a kan harkar mai na shekarar…
Read More
Jerin kadarorin da gwamnatin Buhari za ta cefanar don yin ciko a kasafin kuɗin baɗi

Jerin kadarorin da gwamnatin Buhari za ta cefanar don yin ciko a kasafin kuɗin baɗi

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasar Nijeriya, Muhammadu Buhari ta fidda wani jerin sunayen kadarorin gwamnati guda 25 da za ta sayar don yin cikon giɓin Naira tiriliyan 10.7 a kasafin kuɗin Nijeriya na shekarar 2013. Daga cikin waɗannan kadarorin 25, wasu an sayar da su ne, yayin da wasu kuma aka rarraba hannun jarinsu aka sayar domin dai a samu a yi ciko a wannan kasafin kuɗin da yake neman kasawa. Idan ba a manta ba da ma, Buhari ya tava faɗa cewa, Naira tiriliyan 10.7 ɗin da ta kasa a cikin kasafin kuɗin shekara…
Read More