23
May
Daga AMINA YUSUF ALI Mutumin da ya fi kowa arziki a Afirka, Alhaji Aliko Ɗangote yana buƙatar rancen Naira biliyan 638 don ƙarasa ginin matatar man wacce yake so ya kammala kafin nan kafin shekarar 2023. Kamar yadda jaridar Ingilishi ta News Business News ta rawaito. A wani sakamakon rahoto da kamfanin Fitch wanda ya yi fice wajen bincike a Duniya ya yi hasashen cewa, mutumin da ya fi kowa kuɗi a Afirka, Ɗangote dole zai buƙaci rancen Naira biliyan 638 don kammala matatar man da ya fara ginawa wacce ake sa ran za ta lamushe har Dalar Amurka biliyan…