20
Feb
Daga AMINA YUSUF ALI Kimanin ƙananan manoman rogo guda 100 ne dai 'yan asalin jihar Kwara suka samu tagomashin tallafi daga ƙungiyar tallafi ta Amurka (USAID) don bunƙasa harkar noma. An zavo waɗannan manoman rogo ne daga ƙananan hukumomin jihar Kwara. Inda aka fara da ba su kayan aiki da kuma horaswa a fannin noman zamani domin ingantawa da bunƙasa sana'arsu. Mashiryin shirin ba da tallafin jarin ga manoman rogon, Mista Banjo Famuyiwa, ya bayyana cewa, wannan shirin USAID a Nijeriya ce ta ɗauki nauyinsa tare da haɗin gwiwar AYOSIFAM da ma'aikatar faɗaɗa aikin noma da raya karkara ta jihar…
