Kasuwanci

An kama kayayyakin fasaƙwauri na sama da milyan N100 a Katsina

An kama kayayyakin fasaƙwauri na sama da milyan N100 a Katsina

Daga UMAR M. GOMBE Jami'an Hukumar Yaƙi da Fasaƙwauri ta Nijeriya, sun yi nasarar kama kayayyakin fasaƙwauri da harajinsu ya kai milyan N101,027,350 wanɗanda aka shigo da su cikin ƙasa ta ɓarauniyar hanya a jihar Kastina. Daga cikin kayayyakin da jami'an suka kama a ranar Alhamis da ta gabata har da motoci guda 14 da harajinsu ya kai milyan N91,592,500, haɗa da kayan abinci da sauransu waɗanda harajinsu ya kai N9,434,850. Da yake bayani yayin taron manema labarai a babban ofishin hukumar na yankin Katsina, Shugaban Riƙo na Kwastam na Katsina, DC Dalha Wada Chedi, ya jaddada aniyar Hukumar Kwastam…
Read More
Safarar Ƙwayoyi: NDLEA ta kama ƙosai da aka yi da wiwi a oyo

Safarar Ƙwayoyi: NDLEA ta kama ƙosai da aka yi da wiwi a oyo

Daga UMAR M. GOMBE Hukumar Yaƙi da Tu'ammali da Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) reshen jihar Oyo, ta kama tabar wiwi da aka sarrafa shi kamar ƙosai don ɓadda kama a babbar hanyar Legas zuwa Ibadan da ke jihar. Shugabar NDLEA a jihar Oyo, Mrs Josephine Obi, ita ce ta bayyana haka ga Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) a Ibadan a Talatar da ta gabata. Haka nan, shugabar ta ce sun cafke wani ɗan aike ɗauke da kek ɗin bikin ranar haihuwa wanda aka cusa tabar wiwi mai nauyin 1.2kg a cikinsa. Ta ce hanyoyi da dabarun da masu…
Read More
Almundahana: EFCC ta sake raba Diezani da Dala milyan $153

Almundahana: EFCC ta sake raba Diezani da Dala milyan $153

Daga WAKILINMU Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC), ta sanar da ƙwato Dala milyan $153 daga hannun tsohuwar ministar man fetur, Diezani Alison Madueke, wadda ta tsere zuwa Ƙasar Birtaniya a 2015. Jaridar Vanguard ta ambato shugaban hukumar Abdulrasheed Bawa yana cewa sun ƙwace aƙalla kadarori 80 da kudinsu ya kai Dala milyan $80. A cewar Abdulrasheed, “Muna fatan ganin lokacin da, wataƙila, za ta shigo ƙasar nan, kuma tabbas za mu yi nazari kan abubuwan da ta yi, sannan mu san matakin da za mu ɗauka nan gaba. Tabbas ba mu yi…
Read More
Kwastam ta kama kwantena maƙare da miyagun ƙwayoyi a Legas

Kwastam ta kama kwantena maƙare da miyagun ƙwayoyi a Legas

Daga WAKILINMU Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa da ke yankin Apapa a jihar Legas, ta ce ta kama wani sunduƙin safarar kayayyaki maƙare da ƙwayoyin taramol da kodin waɗanda masu tu'ammali da miyagun ƙwayoyi kan yi amfani da su don shiga yanayi na maye. Bayanan hukumar sun nuna a Litinin da ta gabata jam'ian hukumar suka kama sunduƙin a Legas mai ɗauke da katan-katan na ƙwayar taramol guda 124 da na kodin guda 805. Rahotanni sun ce masu fasa-ƙwaurin sun yi ɓad da sawu ta hanyar ɗora tukwane a kan ƙwayoyin da nufin kada jami'an kwastam su gano shirinsu.…
Read More
Gwamnatin Kaduna ta tsawaita wa’adin tashi da ta bai wa dillalan motoci

Gwamnatin Kaduna ta tsawaita wa’adin tashi da ta bai wa dillalan motoci

Daga WAKILINMU Hukumar Tsarawa da Bunƙasa Birane ta Jihar Kaduna ta amince da roƙon Ƙungiyar Masu Sayar da Motoci ta Jihar Kaduna inda ta buƙaci a ƙara wa mambobinta lokaci game da tashi daga inda suke da aka buƙace su da yi. A wata takardar sanarwa mai ɗauke da kwanan wata 21, Afrilu, 2021 wadda Stephen Baji ya sanya wa hannu a madadin Darakta Janar na hukumar, ta nuna an ƙara wa waɗanda lamarin ya shafa wa'adi zuwa mako guda bayan watan Ramadan, wato 19 ga Mayu, 2021. Da wannan, hukumar ta ce ana buƙatar mambobin ƙungiyar su bi umarni…
Read More
An bai wa kasuwar fanteka ta Kaduna wa’adin mako guda ta tashi

An bai wa kasuwar fanteka ta Kaduna wa’adin mako guda ta tashi

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Raya Birane ta Jihar Kaduna, ta bai wa 'yan kasuwar sabuwar Kasuwar Fanteka wa'adin mako guda a kan su tattara yanasu-yanasu su bar kasuwar. Cikin wata sanarwar mai ɗauke da kwanan wata 22, Afrilu, 2021wadda ta sami sa hannun Babban Daraktan Hukumar, Isma'ila Ummaru Dikko, hukumar ta ce wannan umarni ya soma aiki ne daga ranar da aka bada shi. Hukumar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne daidai da Shirin Sabunta Biranen Jihar na Gwamnatin Jihar. Da wannan gwamnatin jihar ta ce ta bai wa 'yan kasuwar wa'adin kawana bakwai a kan kowa ya kwashe…
Read More
Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki na bilyan N3.1 a Legas

Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki na bilyan N3.1 a Legas

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri na shiyyar Zone A a birnin Legas, ta kama durom 42 maƙare da tokar bindiga (calcium carbide) wanda aka shigo da su cikin ƙasa a sace daga ƙasar Benin. Masana sun yi gargaɗin cewa lamarin fa ba zai yi daɗi ba idan irin wannan makamashi ya faɗa a hannu ɓata-gari. Hukumar Kwastam ta ce makamashin abu ne da za a iya amfani da shi wajen haɗa abubuwa masu fashewa masu ƙarfin tarwatsa gine-gine. Shugaban riƙo na hukumar a Zone A, Compt. Usman Yahaya, ya shaida wa manema labarai cewa baya ga tokar bindigar…
Read More
Babu wata aniyar ƙara kuɗin fetur, cewar NNPC

Babu wata aniyar ƙara kuɗin fetur, cewar NNPC

Daga FATUHU MUSTAPHA Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC) ya jaddada cewa ba shi da wata aniya ta ƙara kuɗin mai nan kusa. Shugaban kamfanin, Mele Kyari, shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya bayar. Kyari ya bada sanarwar haka ne yayin ganawar da ya yi da manema labarai jim kaɗan bayan tattaunawar sirri da suka yi tare da Ƙungiyar Masu Motocin Haya ta Ƙasa (NARTO) da takwararta ta direbobi masu dakon mai (PTD), Litinin da ta gabata a Anuja. NNPC ya nemi ganawa da ƙungiyoyin ne bayan da mambobin PTD suka bai wa NARTO wa'adin mako…
Read More
Za a buɗe hanyar saida sabbin layukan sadarwa 19 ga Afrilu, cewar Gwamnati

Za a buɗe hanyar saida sabbin layukan sadarwa 19 ga Afrilu, cewar Gwamnati

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Tarayya ta bada sanarwar cewa ya zuwa ranar 19 ga Afrilun da muke ciki za a buɗe hanya don bada famar mallakar sabon layin sadarwa (SIM CADR) ga masu buƙata. Gwamnatin ta ce hakan zai tabbata ne bayan kammala tantancewa da kuma tabbatar da kiyaye dokoki yadda ya kamata. Ma'aikatar Sadarwa da Tattalin Arzikin Intanet ita ce ta yi wannan bayani a wata sanarwar manema labarai da ta sami sa hannun hadimini ministan sadarwa, Femi Ademiluyi. Idan dai za a iya tunawa a Disamban 2020 ne gwamnati ta dakatar da saida layukan sadarwa da nufin tantance…
Read More
Ramadan: Saraki Ya Ja Hankalin ‘Yan Kasuwar Nijeriya

Ramadan: Saraki Ya Ja Hankalin ‘Yan Kasuwar Nijeriya

Daga WAKILINMU Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Dakta Abubakar Bukola Saraki ya taya daukacin al’ummar Nijeriya da fadin duniya murnar fara azumin watan Ramadana. Ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da wannan dama wurin yin addu’ar Allah Ya dawo da zaman lafiya, hadin kai da bunkasar Nijeriya. Dakta Saraki ya bayyana haka ne a wata takardar manema labarai wacce Shugaban Sashen yada labarai naa ofishinsa, Yusuph Olaniyonu ya fitar a jiya. Ya ce, watan Ramadan lokaci ne da musulmi za su nemi kusanci ga mahaliccinsu kuma su kyautata alaka a tsakaninsu, musamman yin amfani da…
Read More