Rahoto

Ana nuna damuwa kan yadda Tinubu ba ya kiran Zaman Majalisar Zartarwa

Ana nuna damuwa kan yadda Tinubu ba ya kiran Zaman Majalisar Zartarwa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bai kira taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya ba kwanaki 44 da kammala zaman majalisar da aka gudanar a ranar 28 ga watan Agusta. Hakan ya cigaba da haifar da ayar tambaya kan ko hakan na iya shafar harkokin mulki ko a'a? Majalisar Zartaswa ta Tarayya, wadda shugaban ƙasa ke jagoranta, ita ce Majalisar Zartarwa ta Gwamnatin Tarayyar Nijeriya kuma wani ɓangare na zartarwa. Matsayin tsarin mulki na FEC, kamar yadda yake ƙunshe a cikin Dokar Ayyuka na Ministoci, ita ce ta zama ƙungiya mai ba da shawara ga shugaban ƙasa. A…
Read More
EFCC ta ƙwato sama da Naira Biliyan 27 a hannun tsofaffin gwamnoni da ministoci

EFCC ta ƙwato sama da Naira Biliyan 27 a hannun tsofaffin gwamnoni da ministoci

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta’annati (EFCC) ta Nijeriya ta bayyana cewa, ta ƙwato jimillar Naira 27,184,357,524.52 da dala 19,084,419.33 a wasu shari’o’i uku na karkatar da kuɗaɗe. Daga cikin wannan adadin da aka ƙwato, an gano Naira biliyan 12.7 ne daga hannun mutum ɗaya. Hukumar ta EFCC na binciken tsaffin gwamnoni da tsofaffin Ministoci da wasu jami’an gwamnati a faɗin ƙasar nan a ƙoƙarin da ta ke yi na yaƙi da cin hanci da rashawa. Muƙaddashin shugaban hukumar ta EFCC Abdukarim Chukkol ne ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai…
Read More
Sojoji sun yi wa ’yan bindiga mummunan ta’adi a Zamfara

Sojoji sun yi wa ’yan bindiga mummunan ta’adi a Zamfara

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar Sojojin Nijeriya ta ce, kashe ’yan bindiga fiye da 100 a Ƙaramar Hukumar Maru ta Jihar Zamfara. Wannan na zuwa ne sa'o'i 24 bayan Babban Hafsan Tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa ya umarci dakarun su bi ’yan bindigar har mavoyar su don kawar da su. Rahotanni sun ce sashin sojin sama na rundunar Operation Hadarin Daji ce ta yi wannan aiki, bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa yan bindigar suna kan hanyar su ta kai hari a wani ƙauye. Majiya daga rundunar sojin ta ce, dakarun rundunar sun yi amfani da jirgin sama…
Read More
Ku ceci rai kafin tambayar rahoton ’yan sanda – Minista ga asibitoci

Ku ceci rai kafin tambayar rahoton ’yan sanda – Minista ga asibitoci

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan lafiya da walwalar jama’a, Muhammad Ali Pate, ya buƙaci asibitocin ƙasar da su fifita ceton rayuka fiye da kowane abu. An dai yi ta cece-ku-ce a tsawon shekaru ga asibitocin da ke neman ‘yan sanda su kai rahoton harbin bindiga da waɗanda hatsari ya rutsa da su kafin a fara jinya, lamarin da ya kai ga rasa rayukansu a lokuta da dama. Amma da yake magana a gidan Talabijin na Channels a wani shiri 'Sunrise Daily' a ranar Laraba wanda Blueprint Manhaja ke sa ido a kai, Pate ya koka da wannan lamarin…
Read More
Ƙabilar Kibishi: Masu banƙare wa budurwa leɓe da sunan ado

Ƙabilar Kibishi: Masu banƙare wa budurwa leɓe da sunan ado

Masu iya magana na cewa "Allah ɗaya, gari bamban". Su dai waɗannan bayin Allah suna rayuwa ne a yammacin kogin ‘Omo’ da ke kudu-maso-yammacin Habasha, ana kiransu da ‘Kibishi’. Bincike ya nuna cewa su dai waɗannan mutane makiyayane, sannan a kan gane yawan dukiyar kowane gida ta hanyar la’akari da yawan dabbobin da suka mallaka. Addini: Waɗannan mutane suna da abin bauta wanda suke yi masa laƙabi da ‘Tuma’. Sun yi imani cewar shi dai wannan Tuma ya kasancene a cikin sararin samaniya, bugu da ƙari mutanen sun yi imani da al’matsutsai da kuma ifiritai, sun kuma yi imani da…
Read More
Mutanen da suka fi taka rawar gani wajen samun ’yancin Nijeriya

Mutanen da suka fi taka rawar gani wajen samun ’yancin Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jaridar Blueprint Manahaja ta yi bincike daga wurare daban-daban dangane da mutanen da suka fi taka rawa wajen fafutukar nema wa Nijeriya ’yanci. Mun tattaro mutum bakwai waɗanda suka yi fice wajen samun ’yancin. Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato Yuni 12, 1910 - Janairu 15, 1966): An haifi Sir Ahmadu Bello a garin Rabbah na jihar Sokoto da ke arewacin Nijeriya. Sardauna na daya daga cikin jagororin Nijeriya da suka yi fice a duniya. Ahmadu Bello ya riqe sarautar Sardaunan Sokoto kuma ya jagoranci jam'iyyar Northern People's Congress (NPC), inda ya mamaye harkar siyasar kasar a…
Read More
Rasuwar Jaruma Binta Ola: Ba rabo da gwana ba…

Rasuwar Jaruma Binta Ola: Ba rabo da gwana ba…

Daga UMAR GARBA, a Katsina A ranar 3 ga Oktobo, 2023, Allah ya karɓi rayuwar shahararriyar jarumar Kannywood kuma ɗaya daga cikin mata da suka fara gudanar da wasan kwaikwayo a Arewacin Nijeriya, wato Hajiya Binta Suleiman, wadda aka fi sani da Hajiya Binta Ola Katsina. Marigayiya Hajiya Binta ta fara wasan kwaikwayo tun lokacin da ake wasan daɓe, wato kafin zuwan wasan kwaikwayo na talabijin da kuma fina finan zamani irinsu Kannywood.Wakilin Jaridar Blueprint Manhaja a Katsina, Umar Garba ya samu damar halartar gidan marigayiyar a Sabuwar Unguwa cikin garin Katsina inda iyalanta ke zaman ta'aziya. An haifi Hajiya Binta…
Read More
Tarihin juyin mulkin soja na farko a Nijeriya

Tarihin juyin mulkin soja na farko a Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Daga ranar 15 zuwa 16 ga watan Janairun shekarar 1966, wasu ƙananan hafsoshin soja masu muƙaman manjo sun aiwatar da juyin mulkin soja na farko wanda suka fara kitsawa tun a watan Agustar shekarar 1965. Waɗannan ƙananan hafsoshin soja, sun yi ikirarin cewa sun shirya juyin mulkin ne a saboda a cewarsu, shugabannin da ke jagorancin ƙasar sun nuna zarmiya, inda suka ce ministocin gwamnati suna sace kuɗaɗen baitul-mali domin amfaninsu. Sai dai kuma a wani ɓangare, akwai masu ikirarin cewa wannan juyin mulki na ƙabilanci ne a saboda daga cikin sojoji 8 da suka ƙulla…
Read More
Ranar Samun ‘Yancin Kai: Cikakken Jawabin Shugaba Tinubu

Ranar Samun ‘Yancin Kai: Cikakken Jawabin Shugaba Tinubu

Jawabin mai girma, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCRFR, kuma Babban Kwamandan Askarawan Nijeriya a cikar Jamhuriyar Tarayyar Nijeriya shekaru 63 da samun ‘yancin kai, ranar Lahadi, 1 ga Oktoba, 2023 ‘Yan uwana ‘yan Najeriya, Ina farin cikin yi muku jawabi a yau, ranar cikar ƙasarmu shekaru 63 da samun ‘yancin kai, a matsayina na shugaban ƙasarmu mai albarka, kuma zallar ɗan uwanku ɗan Nijeriya. A wannan rana mai muhimmanci mai cike da fatan alheri, muna jinjina ga iyayenmu da suka kafa Nijeriya, mazansu da matansu. Ba don su ba, da ba a samu ƙasar Nijeriya ba. Gwagwarmayarsu, sadaukarwarsu, da…
Read More
Sarkin Borin Kabi ya zama Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa

Sarkin Borin Kabi ya zama Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu bayar da maganin gargajiya ta ƙasa ta zaɓi Yusuf Abubakar a matsayin Garkuwan masu maganin gargajiya na ƙasa. Tawagar ta masu maganin gargajiya ta ƙasa da ta reshen jihar Kebbi ta iso fadar Mai Martaba Sarkin Kabin Argungu Alhaji Sama'ila Muhammadu Mera a ƙarƙashin jagoranacin Malam Bala Hassan inda suka tabbatar wa Masarautar Sarkin Kabin Argungu da cewa wannan zaɓen Allah ne, sun zaɓe shi ne tun daga mataki na ƙasa ba tare da wata jayayya ba saboda la'akari da irin rawar da ya ke takawa a wannan ɓangaren. Da ya ke…
Read More