16
Jul
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da tallafin karatu a ƙasashen ƙetare ga nakasassu a jihar. Gwamnati ta ce nakasassu za su ci gajiyar shirin gwamnatin jihar na bayar da tallafin karatu a ƙasashen ƙetare muddin sun mallaki abubuwan da ake buƙata. Kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana hakan a ranar Alhamis. A cewar Kwamishinan, "Yana daga cikin manufofin gwamnati mai ci na tabbatar da adalci da samun daidaiton samun ilimi ga kowane ɗan jihar, daidai da yarjejeniyar ƙasa da ƙasa." "Tabbas za mu bada tallafin karatu ga waɗanda ke da…
