Rahoto

Sababbi da tsofaffin gwamnoni sun kai wa Buhari ziyarar ban-gajiya

Sababbi da tsofaffin gwamnoni sun kai wa Buhari ziyarar ban-gajiya

Daga UMAR GARBA a Katsina Wata ƙasaitacciyar tawaga da ta ƙunshi gwamnoni masu ci da kuma tsofaffi, ta kai wa tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ziyarar ban-gajiya a mahaifarsa dake Daura ta Jihar Katsina a jiya Alhamis, 1 ga Yuni, 2023. Daga cikin gwamnonin akwai sabon gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Raɗɗa, Dapo Abiodun na Jihar Ogun, Babajide Sanwo Olu na Jihar Legas, Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa, Bala Muhammad na Jihar Bauchi, Hope Uzodinma na Jihar Imo da mataimakin gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdulsalam. A sanarwar da ofishin babban mataimaki na musamman akan kafafen yaɗa labarai na zamani ya fitar,…
Read More
Zargin amfani da takardun ƙarya: Kotu ta yi barazanar kulle Fani-Kayode

Zargin amfani da takardun ƙarya: Kotu ta yi barazanar kulle Fani-Kayode

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kotun hukunta manyan laifuka da ke zamanta a Ikeja, Legas, ta ce, za ta bayyana tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani-Kayode, a matsayin wanda ake nema ruwa-a-jallo idan har ya kasa bayyana a rana mai zuwa da ta ɗage sauraron shari’arsa. Mai shari’a Olubumni Abike-Fadipe ya koka kan rashin bayyanar da wanda ake tuhuma a kai a kai, inda ya bayyana cewa a karon ƙarshe da ya kai kotu shi ne ranar 4 ga watan Nuwamba, 2022. Fani-Kayode dai yana fuskantar shari’a kan tuhume-tuhume 12 da suka haɗa da amfani da takardun ƙarya, yin amfani…
Read More
Buhari ya bai wa Tinubu lambar girmamawa mafi daraja ta Nijeriya

Buhari ya bai wa Tinubu lambar girmamawa mafi daraja ta Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Muhammmadu Buhari ya bai Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, lambar girma mafi daraja ta ƙasar wato 'Grand Commander of the Order of the Federal Republic' (GCFR). Hakazalika, Buharin ya bai wa mataimakin shugaban ƙasar mai jiran-gado, Kashim Shettima lambar girmamar ta biyu a daraja wato GCON 'Grand Commander of the Order of Niger'. Shugaban ya ba su lambobin da kuma takardun mulki ne a Abuja, a shirye-shiryen da ake yi na rantsar da sabuwar gwamnati, ranar Litinin 29 ga watan nan na Mayu, bayan kammala wa’adinsa na biyu na shekara huɗu-huɗu. Za a…
Read More
Dalilin da ya sa al’ummar Gbagyi ke goyon bayan rantsar da Tinubu

Dalilin da ya sa al’ummar Gbagyi ke goyon bayan rantsar da Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Honorabul Cesnabmihilo Dorothy Nuhu-Aken'ova ta bayyana cewa ƙabilun Gbagyi na goyon bayan shirin rantsar da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a matsayin Shugaban Ƙasa a ranar 29 ga watan Mayu. A cewar babbar kodinetan Ƙungiyar Magoya Bayan Bola Ahmed Tinubu a ranar Gbagyi wanda aka yi a Unity Fountain, wurin taron Tinubu Hangout da Ƙungiyar Goyon Bayan Tinubu (TSG) ta shirya a Abuja. A cewarta, "A madadin 'yan ƙabilar Gbagyi masu son zaman lafiya da karamci na Nijeriya da mazauna ƙasashen waje, da kuma 'yan ƙabilar Gbagyi musamman mazauna Babban Birnin Tarayya, Ina taya zaɓaɓɓen…
Read More
Jam’iyyar NNPP na zargin Ganduje da sayar wa da ɗansa kadarorin gwamnati

Jam’iyyar NNPP na zargin Ganduje da sayar wa da ɗansa kadarorin gwamnati

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Jam’iyyar NNPP a Kano, ta zargi gwamnatin APC ƙarƙashin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, da siyar da wasu kadarori mallakin gwamnatin jihar. Zargin wanda ake kallon gwamnatin jihar na siyar da kadarorin ga ɗan gwamna ba bisa ƙa’ida ba, abin da Jam'iyyar NNPP ta ce ba za ta lamunta ba. Har ma jami’iyyar ta ce za ta yi bincike da tabbatar da hukunci da zarar sun karɓi mulkin Kano a ranar 29 ga watan Mayu. Jawabin hakan na zuwa ne ta bakin shugaban kwamitin karɓar mulkin jihar Kano na Jam’iyyar NNPP Abdullahi Baffa Bichi, yayin wata…
Read More
N-YED ta tallafa wa marayu da kayan masurufi a Kano

N-YED ta tallafa wa marayu da kayan masurufi a Kano

Daga RABI'U SANUSI a Kano A ranar Lahadin da ta gabata ne ƙungiyar tallafa wa matasa da marayu da aka fi sani da N-YED ƙarƙashin jagorancin Kwamared Abdulsalam Haruna, ta gabatarwa da marayun dake gidan yara na Ƙaramar Hukumar Nasarawa Tallafin kayayyaki masu ɗumbin yawa dan tabbatar masu da irin gatan da suke da shi. Da yake yi wa manema labarai jawabi yayin taron, Shugaban ƙungiyar na N-YED, Kwamared Abdulsalam Haruna, ya ce lokacin da ya fara tunanin kafa wannan ƙungiya bai tunanin za ta zama haka ba, ya ce duk abin da mutum ya sa niyya a rayuwarsa in…
Read More
Yadda aka gudanar da addu’o’in tunawa da ‘Yar’adua bayan cika shekara 13 da rasuwa

Yadda aka gudanar da addu’o’in tunawa da ‘Yar’adua bayan cika shekara 13 da rasuwa

Daga UMAR GARBA a Katsina Gamayyar ƙungiyoyi masu goyon bayan jam'iyyar PDP, sun shirya taron addu'a gami da karatun Al'ƙur'ani mai girma don tunawa da tsohon Shugaban Ƙasar Nijeriya, marigayi Malam Umaru Musa 'Yar'adua a masallacin hedikwatar jam'iyyar PDP dake Katsina. Taron addu'o'in na zuwa ne bayan da marigayi 'Yar'adua ya cika shekaru 13 da rasuwa a ranar Juma'a, 5 ga watan Mayu, 2023. Da yake jawabi a wajen taron addu'ar, Shugaban kwamitin riƙon ƙwarya na jam'iyyar wanda ya samu wakilcin Lawal Rufa'i Safana, ya bayyana cewar, shirya taron addu'o'in ya zama wajibi duba da gagarumin cigaba da marigayin ya…
Read More
Ɗan jarida, Jibrin Ndace ya wallafa littafi uku kan matsalar tsaron Nijeriya

Ɗan jarida, Jibrin Ndace ya wallafa littafi uku kan matsalar tsaron Nijeriya

Daga AISHA ASAS Fitaccen ɗan jaridar nan kuma mai sharhi akan al'amuran jama'a, sannan kuma wanda ya samu lambar yabo da dama a Nijeriya, Jibrin Baba-Ndace, na shirin ƙaddamar da littafai uku, wanda zai bayyana ‘Yaƙin Sojojin Nijeriya da ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP a Arewa maso Gabas. Littattafan suna ɗauke da taken: Walking the War Front with Lt. Gen. TY Buratai," “Duty Call Under Buratai's Command” da kuma “The Lonely Grave and Other Poems__ an anthology.' A wata sanarwa da Mista Ndace ya fitar, ya ce za a gudanar da taron bajekolin littafan ne a babban birnin tarayya…
Read More
Har yanzu ban dawo hayyacina ba kan abinda Hakimi ya min – Hiba

Har yanzu ban dawo hayyacina ba kan abinda Hakimi ya min – Hiba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Matar Achraf Hakimi, ɗan ƙwallon ƙungiyar PSG kuma ɗan asalin ƙasar Moroko, wato Hiba Abouk, ta ce, abinda Hakimi ya mata ta kadu sosai, wanda hakan ya sa har yanzu ba ta dawo hayyacinta ba. A shekarar 2020 ne dai suka yi aure da Hakimi inda a yanzu suna da yara biyu, amma sun rabu, matar ta nemi Hakimi ya ba ta rabin dukiyarsa, amma sai lauyanta ya gano Hakimi da sunan mahaifiyarsa ya ke ajiye kadarorinsa. A zantawar da ta yi da kafar Elle, Hiba ta bayyana cewa rabuwarsu ba abu ne me sauƙi ba…
Read More
Wasu ‘yan takarar siyasar Nijeriya da suka rasa rayukansu gab da zaɓen 2023

Wasu ‘yan takarar siyasar Nijeriya da suka rasa rayukansu gab da zaɓen 2023

Daga AMINA YUSUF Wasu daga cikin waɗannan 'yan takarar ana gab da zaɓen 2023 'yan bindiga suka halaka su, wasu daga ciki kuma suka rasu ta hanyar wasu dalilan. Halin rashin tsaron da ƙasar nan ya yi sanadiyyar kisan ba wai 'yan takarar kaɗai ba har ma da masu tsaron lafiyarsu. Haka ma magoya bayansu sun sha shiga irin wannan ibtila'in a wannan kakar zaɓen. Rahotanni dai suna nuna zargin cewa, waɗannan 'yan siyasa vangaren da suke adawa ne da su suke kashe su saboda suna ganinsu a matsayin barazana ga siyasarsu. Duk kuwa da cewa, a cikin 'yan kwanakin…
Read More