Rahoto

Ku jure zafin ƙarancin Naira don zai wuce – Roƙon Buhari ga ’yan Nijeriya

Ku jure zafin ƙarancin Naira don zai wuce – Roƙon Buhari ga ’yan Nijeriya

*An bankaɗo Naira Tiriliyan 2.1 da aka ɓoye Daga AMINA YUSUF ALI Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana adadin yawan Nairorin da aka ɓoye waɗanda gwamnatinsa ta bankaɗo tun da CBN ya fara dokar canjin fasalin takardun Naira a Nijeriya. Sannan kuma ya roƙi 'yan Nijeriya a kan su zama masu haƙurin jure wahalhalun da dokar ta samar. A cewar Buhari, gwamnaninsa ta samu nasarar bankaɗo aƙalla Naira tiriliyan 2.1 aka ɓoye ba a bankuna ba. Tun daga lokacin da gwamnatin ta sanya dokar sauya fasalin kuɗi.  Shugaban ƙasar ya yi wannan jawabi a ranar Alhamis ɗin 16 ga watan Fabrairu, 2023…
Read More
Bankuna sun zama gurare mafi hatsari a Nijeriya, inji Birtaniya

Bankuna sun zama gurare mafi hatsari a Nijeriya, inji Birtaniya

*Ta gargaɗi ’yan ƙasarta da su guji zuwa bankuna Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙasar Birtaniya ta sake fitar da wata sanarwar bada shawara ga 'yan ƙasarta mazauna Nijeriya game da zuwa bankuna da ziyartar wasu jihoji a faɗin Nijeirya, na biyu a cikin watanni huɗu. A cikin bayanin da aka sabunta ranar Laraba, Ofishin Harkokin Waje, FCDO, ya yi gargaɗi ga ’yan ƙasar Birtaniya a Nijieriya game da zuwa wuraren da akwai bankuna da ATM. An yi nuni da cewa sake fasalin Naira da babban bankin Nijeriya ya yi tare da fitar da sabbin takardun kuɗi na N200, N500 da…
Read More
Mutane 25,000 suka ɓace sakamakon rikici a Arewa maso Gabas Nijeriya – ICRC

Mutane 25,000 suka ɓace sakamakon rikici a Arewa maso Gabas Nijeriya – ICRC

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotannin dai sun bayyana cewa, aƙalla mutane 25,000 ne suka yi bayan dabo a sakamakon rikice-rikicen da aka sha fama da su a Arewa maso gabashin Nijeriya.  Wannan rahoto ya fito daga masu ruwa da tsaki a kan masu taimaka wa iyalan waɗanda suka vace ɗin. A yayin wani taro da suka gabatar ranar Litinin ɗin da ta gabata don tabbatar da cewa ba a mance da iyalan waɗanda suka ɓace ɗin ba wajen tallafin da ake bayarwa a ƙasar nan.   Wannan jawabi dai kwamitin ƙungiyar Red Cross ta ƙasa (ICRC) shi ya wallafa shi, wanda…
Read More
Rawar da Ma’aikatar Jinƙai ta taka a yaƙi da rashin tsaro, cin zarafin yara da gurɓata muhalli

Rawar da Ma’aikatar Jinƙai ta taka a yaƙi da rashin tsaro, cin zarafin yara da gurɓata muhalli

PAUL OKAH ya rawaito cewa, Ma'aikatar Jinƙai da Kawar da Annoba da Gina Al'umma  (FMHADMSD) ta kasance a sahun gaba wajen yaqar rashin tsaro a Nijeriya. Hukumar kuma ta a ƙoƙarin ganin bayan ɗaukar yara 'yan ƙasa da shekaru 18 don gabatar da  ayyukan ta'addanci da ƙaddamar da kwamiti a kan kwashe gutsattsarin abubuwan fashewa da suka gurɓata muhalli suke illatar da al'umma. Akwai wani azanci da yake cewa, harkar tsaro nauyi ne a kan kowa da kowa, saboda haka, Ma'aikatar ta haɗa gwiwa da masu ruwa da tsaki don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al'umma a sassa daban-daban…
Read More
Samar da maƙabartar Kiristoci a Bauchi: Gwamnati ta buƙaci jama’a su kai zuciya nesa

Samar da maƙabartar Kiristoci a Bauchi: Gwamnati ta buƙaci jama’a su kai zuciya nesa

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Gwamnatin Jihar Bauchi ta buƙaci al'ummomin Musulmi da na Kiristoci mazauna unguwannin Yolan Bayara dake cikin gundumar Miri ta Ƙaramar Hukumar da su riƙa kai wa zukatunsu nesa da zummar wanzar da zaman lafiya, mutunta juna, yakana, tare da shure bambance-bambance dake a tsakanin domin nusar da cigaban jiha da ƙasa baki ɗaya. Mai bai wa gwamnan jiha shawarwari akan kafofin watsa labarai da yayatawa, Mukhtar Gidado Mohammed shine ya gabatar da wannan buƙata ta gwamnatin jiha dangane da taƙaddama dake gudana a tsakanin al’ummomin guda biyu, yana mai cewar, filin maƙabarta da ake taƙaddama…
Read More
Ministar Jinƙai, Sadiya Farouq, ta jaddada ƙudirinta na yin aiki da ƙungiyar haɗin gwiwar ma’aikatar

Ministar Jinƙai, Sadiya Farouq, ta jaddada ƙudirinta na yin aiki da ƙungiyar haɗin gwiwar ma’aikatar

Daga WAKILINMU Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwar Jama’a, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta jaddada ƙudirinta na kyautata hulɗar aiki da ƙungiyar haɗin gwiwa domin aiwatar da aikin ma’aikatar yadda ya kamata. Ministar ta bayyana hakan ne a yayin wani biki da ma'aikatar ta shirya mai taken: 'Makon Farko na Ƙungiya' a ranar 22 ga watan Disamba, 2022, a ɗakin taro na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya dake Abuja.  Ministar wadda ta samu wakilcin babban sakatare, Dr Nasir Sani Gwarzo, ta yaba wa ƙungiyar bisa aiki tuƙuru da kuma mutunta jami'an gudanarwa. Ta bayyana cewa, horarwa haƙƙi ne ga dukkan…
Read More
Ba mu da ikon hana mahandama sake mallakar kadarorinsu da EFCC ta yi gwanjonsu – Majalisar Wakilai

Ba mu da ikon hana mahandama sake mallakar kadarorinsu da EFCC ta yi gwanjonsu – Majalisar Wakilai

Daga AMINA YUSUF ALI Kwamitin Majalisar Wakilai na Musamman kan tantance kadarorin da aka sata na gwamnati masu motsawa da girkakku tun daga shekarar 2000 zuwa 2022 sun bayyana cewa, ba su da ikon hana barayin gwamnati daga sake mallakar kadarorinsu da gwamnati ta ƙwace ba, a wannan gwanjo da ake yi na dukkan kadarorin da gwamnati ta ƙwace daga jami'an gwamnati da suka yi sama-da-faɗi da su.  Shugaban kwamitin gaggawa na 'yan majalisar na gwanjon kayan gwamnati Honarabul Adejoro Adeogun ya bayyana cewa, da ma tuntuni kwamitin da yake jagoranta ya faɗa wa hukumar yaƙi da cin Hanci da…
Read More
Rashin amsa gayyatar ‘yan takara ba zai sa mu yi ƙasa a gwiwa ba – CITAD

Rashin amsa gayyatar ‘yan takara ba zai sa mu yi ƙasa a gwiwa ba – CITAD

Daga BABANGIDA S. GORA a Kano Dangane da cigaba da gayyato 'yan takarkarun kujerar majalisar jiha da tarayya da jama'a ke yi don miqa qudurorin su ga 'yan takarar da suka fito don wakiltar su. Ita ma karamar hukumar Dala dake jihar Kano ta bi bayan 'yan uwanta don gayyato 'yan takarar daga kowa ce jam'iyya ɗan takara yake madamar ya fito da nufin ya wakilci wannan ƙaramar hukumar ta Dala. A haka ne ma cikin irin ƙoƙarin al'ummar ne ranar Talatar nan suka gudanar da taron jin ra'ayoyin 'yan takarar tare da miƙa nasu buƙatun don kawo cigaba, wanda…
Read More
Tsaro, lafiya, noma da sufuri sun samu kaso mafi rinjaye a kasafin 2023

Tsaro, lafiya, noma da sufuri sun samu kaso mafi rinjaye a kasafin 2023

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Laraba ne Majalisar Dokokin Nijeirya ta ƙara ƙudirin kasafin kuɗin shekarar 2023 daga Naira tiriliyan 20.51 zuwa 21.82 sannan ta amince da shi. Kwamitocin kasafin kuɗi na Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun ce ƙarin Naira tiriliyan 1.3 na kasafin kuɗin ya biyo bayan ƙarin kuɗaɗen da aka ware wa hukumar ƙidaya ta ƙasa gabanin ƙidayar jama’a a shekarar 2023 da kuma Naira tiriliyan 173 da aka ware wa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, gabanin babban zaɓen 2023. Rundunar sojojin Nijeriya da rundunar 'yan sandan Nijeriya, da ma'aikatun noma, lafiya, jiragen sama,…
Read More
Wacce rawa Ma’aikatar Jinƙai ta taka wajen magance talauci da zaman banza?

Wacce rawa Ma’aikatar Jinƙai ta taka wajen magance talauci da zaman banza?

Duk da rahoton binciken da aka samo kwana-kwanan nan daga Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa  (NBS) cewa, sama da 'yan Nijeriya miliyan 133 ne suke rayuwa cikin talauci, amma Ma'aikatar Jinqai da Agaji tana cigaba da jajircewa akan ƙudurinta na tsamo matasa daga ƙangin talauci da rashin aikin yi. Ma'aikatar tana gudanar da ƙoƙarin nata ne ta hanyar Shirin N-Knowledge da shirin raya al'umma (NSIP) da sauran horarwa daban-daban. Rahoton na Hukumar NBS cewar mutane sama da miliyan 133 ne a Nijeriya suke fama da talauci ya zama kamar wani ƙarin ƙaimi a wajen ma'aikatar ta jinƙai kuma ya zaburar da…
Read More