Rahoto

Tinubu ya caccaki Obasanjo kan batun matatar man Fatakwal

Tinubu ya caccaki Obasanjo kan batun matatar man Fatakwal

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya caccaki tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo kan kalaman da ya yi kan matatar mai da ke garin Fatakwal na Jihar Ribas. A wata hira da ya yi da manema labarai kwanan nan, Obasanjo ya jaddada cewa,  matatun man ƙasar ba za su taɓa yin aiki yadda ya kamata ba matuqar sun ci gaba da zama a ƙarƙashin gwamnati. “Wani ya gaya min cewa Tinubu ya ce matatun man za su yi aiki a watan Disamba. Na ce wa mutumin matatun man ba za su yi aiki ba. Wannan ya samo…
Read More
Yadda aka yi jana’izar Sheikh Giro Argungu a Kebbi

Yadda aka yi jana’izar Sheikh Giro Argungu a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi   An yi jana’izar shahararren malamin addinin Islama ɗin nan, Sheikh Abubakar Giro Argungu, a mahaifarsa ta Argungu da ke Jihar Kebbi. Shehin malamin ya rasu ne a Asibitin Gwamnatin Tarayya (FMC)  dake garin Birnin Kebbi, Babban Birnin Jihar Kebbi, bayan gajeriyar jinya. Kafin rasuwarsa shi ne Babban Sakataren Tsare-tsare na Ƙungiyar Izala ƙarƙashin jagoranacin Sheikh Bala Lau dake da sharkwata a Kaduna. Malam Giro ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen yaɗa addinin Musulunci da ya yi sanadiyyar ɗaruruwan mutane karvar addinin Musulunci ciki da wajen Nijeriya. Malam Giro ya rasu ne yana da shekaru 61, inda…
Read More
Musawa za ta iya fuskantar ɗauri saboda karya dokar liƙi da Naira

Musawa za ta iya fuskantar ɗauri saboda karya dokar liƙi da Naira

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An samu sabon Ministar Fasaha, Al'adu, da Tattalin Arziki tana liƙi da kuɗin Naira. Musawa tana cikin wasu ministoci 44 da aka rantsar a ranar Litinin, 21 ga watan Agusta, 2023, don zama mambobin majalisar ministocin shugaba Bola Ahmed Tinubu. Da yammacin ranar ƙaddamar da bikin, wani hoton bidiyo ya nuna Musawa tana watsawa wata mawaƙiya takardar Naira a wani taron murnar nasarar da ta samu na zama minista. Dokar ta ci karo da sashe na 21 na dokar babban bankin Nijeriya (CBN) na shekarar 2007. Dokar ta CBN ta bayyana cewa yin ta’ammali na liqi…
Read More
Wike ya bada umarnin kama mamallakin ginin da ya rushe a Abuja bayan ceto mutane 37

Wike ya bada umarnin kama mamallakin ginin da ya rushe a Abuja bayan ceto mutane 37

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An ceto mutane 37, wasu biyu kuma sun samu raunuka yayin da ake fargabar wasu da dama sun maƙale a lokacin da wani gini ya rufta a titin Legas da ke unguwar Garki a Abuja. Jaridar Blueprint Manhaja ta tattaro cewa Kakakin Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Tarayya (FEMA) Nkechi Isa ta tabbatar da faruwar lamarin da safiyar ranar Alhamis. “Ana ci gaba da aikin ceto yayin da ake ci gaba da neman ƙarin waɗanda abin ya shafa a wurin da ginin ya rufta a titin Legas, a ƙauyen Garki daura da ofishin ‘yan…
Read More
Yanzu ake ganin irin nasarar jajircewar da NEPU ta yi kan talaka – Farfesa Kamilu Fagge

Yanzu ake ganin irin nasarar jajircewar da NEPU ta yi kan talaka – Farfesa Kamilu Fagge

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano An gudanar da taro karo na bakwai a kan ranar tunawa da kafa Jam'iyyar NEPU shekaru 73 da suka gabata da cibiyar nazarin dimukraɗiyya ta Jami'ar Bayero ta gudanar a gidan Mumbayya a ranar Talata. Da yake gabatar da jawabi a yayin taron, Farfesa Kamilu Sani Fagge ya bayyana cewa siyasar aƙida ce ke biyan buqatun jama'a, duk da jam'iyyar NEPU ba ta kafa gwamnati ba amma ta tsaya ta jajirce da yanzu ake ganin nasarar da ta cimma. Ya ce dagewar da NEPU ta yi ne ta ƙwato wa talaka 'yancinsa, yanzu abubuwan da…
Read More
Matsalar tsaro: Gwamnoni sun shiga ganawar gaggawa da Ribadu

Matsalar tsaro: Gwamnoni sun shiga ganawar gaggawa da Ribadu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) ta gudanar da taron gaggawa a sakatariyar ƙungiyar da ke Abuja a daren Laraba, inda Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaron Ƙasa, Malam Nuhu Ribadu, ya halarci taron. Duk da cewa an hana ’yan jarida su ba da labarin buɗe taron, ajandar da aka raba wa gwamnonin sun nuna cewa batutuwan da suka shafi harkokin tsaro na jihohi da na ƙasa ne zai sa a gaba a tattaunawar. Sauran abubuwan da aka jera domin tattaunawa sun haɗa da tallafin man fetur da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya cire, da…
Read More
’Yan bindiga sun kashe mutane 21 a Jihar Filato

’Yan bindiga sun kashe mutane 21 a Jihar Filato

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wasu ’yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba sun kashe mutane 21 a Baton da Rayogot da ke gundumar Heipang a Ƙaramar Hukumar Barkin Ladi ta Jihar Filato. Rwang Tengwong, sakataren yaxa labarai na Ƙungiyar Berom Youth Movement, BYM, wata ƙungiyar al’adu da zamantakewa, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Alhamis a Jos. Mista Tengwong ya ce harin da aka kai kan al’umomin ya faru ne da ƙarfe 1:26 na safiyar ranar Alhamis, kuma ya yi sanadin jikkata wasu mutane bakwai. Tengwong, wanda ya yi tir da hare-haren…
Read More
Yadda makarantu 79 a Misau ta Jihar Bauchi ke fuskantar ƙarancin malamai

Yadda makarantu 79 a Misau ta Jihar Bauchi ke fuskantar ƙarancin malamai

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Aƙalla makarantu guda 79 ne dake cikin Ƙaramar Hukumar Misau ta Jihar Bauchi suke fuskantar matsanancin ƙarancin malamai masu koyarwa, inda kowacce ɗaya daga cikin waɗannan makarantu take da malami guda ɗaya tal dake karantar da dukkanin darussan ilimi a makarantar sa. Wannan furuci mai ban tsoro da firgitarwa ya fito ne daga bakin Darakta mai kula da lamurran makarantu na Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Bauchi, Korijo Buba Umar a yayin zaman wani zauren tattaunawa na 'yan jaridu na kwanaki biyu da Hukumar Kula da Asusun Yara ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ta…
Read More
Cire tallafin fetur: Gwamnatin Tarayya ta ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya a cikin wata biyu – Tinubu

Cire tallafin fetur: Gwamnatin Tarayya ta ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya a cikin wata biyu – Tinubu

• Ya ce za a raba motocin sufuri 3000 a jihohi• Ya ce sauran abubuwan jin daɗi na zuwa nan ba da jimawa ba Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana a ranar Litinin cewa a cikin ƙasa da watanni biyu Gwamnatin Tarayya ta ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya sakamakon cire tallafin man fetur. Shugaban ya bayyana haka ne a wani jawabi da aka watsa wa ‘yan Nijeriya kan ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta a fannin tattalin arziki. “A cikin ƙasa da watanni biyu, mun ajiye sama da Naira tiriliyan ɗaya da za…
Read More
Nijeriya ta samu tallafin Dala miliyan 9.3 don ƙarfafa allurar rigakafin Covid-19

Nijeriya ta samu tallafin Dala miliyan 9.3 don ƙarfafa allurar rigakafin Covid-19

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ma'aikatan lafiya suna shirya rigakafin Moderna Coronavirus (COVID-19) da za a gudanar a sabuwar cibiyar rigakafin jama'a da aka buɗe a Tokyo, Japan, Mayu 24, 2021. Gwamnatin Tarayya ta samu tallafin Dalar Amurka miliyan 9.3 daga Ƙungiyar Global Initiative for Vaccine Equity, CanGIVE, don bunƙasa isar da allurar rigakafin COVID-19 da ƙarfafa tsarin kiwon lafiya a ƙasar. Babban Kwamishinan Kanada, Amb. Jamie Christoff, ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, yayin ƙaddamar da CanGIVE a Nijeriya. Ma’aikatar lafiya ta tarayya, tare da haɗin gwiwar Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta Ƙasa…
Read More