Labarai

Iƙirarin ASUU cewa sama da lakcarori 200 sun yi murabus a KASU ba gaskiya ba ne, inji VC Farfesa Musa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mataimakin Shugaban Jami'ar Jihar Kaduna (KASU), Farfesa Abdullahi Musa, ya yi watsi da iƙirarin Ƙungiyar Malaman Jami'o'i rushen jami'ar (ASUU-KASU) na cewa sama da malamai 200 sun ajiye aikinsu kan rashin kyawun yanayin aiki, yana mai bayyana zargin a matsayin abin ruɗarwa da bai yi kama da haƙiƙanin al'amari ba. Rahotanni sun bayyana cewa, wannan faɗi-in-faɗa ta samo asli ne bayan wani taron manema labarai da ASUU-KASU ta kira, inda ta yi zargin sama da farfesoshi da lakcarori 200 sun bar aiki da jami'ar bisa rashin kyawun yanayin aiki da gazawar cika alƙawarin aiwatar…
Read More
Yari ya bada tallafin N12.5M ga zawiyyah 43 a Zamfara

Yari ya bada tallafin N12.5M ga zawiyyah 43 a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Sanata Abdulaziz Yari Abubakar, mai wakiltar mazaɓar Zamfara ta Yamma, ya bayar da gudunmuwar shanu 43, buhunan shinkafa 356 da Naira miliyan 12,500,000 ga zawiyyah guda 43 da ke faɗin ƙananan hukumomin jihar Zamfara 14 domin gudanar da bikin Mauludi. A wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Hon. Ibrahim Muhammad, shugaban kwamitin yaɗa labarai, Sanata Yari ya buƙaci al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan damar wajen yi wa Nijeriya addu’ar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa, tare da roƙon Allah ya ba Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa jagora. An…
Read More
Gwamna Dauda Lawal ya lashe kyautar Blueprint ta 2026

Gwamna Dauda Lawal ya lashe kyautar Blueprint ta 2026

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau An karrama Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal da kyautar ingancin gudanar da albarkatun jama'a da bayyana gaskiya ta 2026 ta Jaridar Blueprint. Kakakin Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ga 'yan jarida a Gusau ranar Talata. "Gwamnan ya sami kyautar ne a ranar Talata a taron shekara-shekara na muhadara ta takwas ta Jaridar Blueprint, jerin tasiri da kyaututtuka, wanda aka gudanar a cibiyar taro ta duniya ta Bola Ahmed Tinubu, Abuja". Jigon taron na wannan shekarar shine "Ƙalubalen tsaro da mutuncin zaɓen Najeriya na 2027." Da…
Read More
Sarkin Katsina ya sanar da naɗin sabbin Hakimai guda takwas

Sarkin Katsina ya sanar da naɗin sabbin Hakimai guda takwas

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Fadar Mai Martaba Sarkin Katsina, Alhaji (Dakta) Abdulmumini Kabir Usman ta sanar da naɗin sabbin hakimai guda takwas a masarautar Katsina. Sarki Usman, ya umarci sakataren majalisar masarautar Katsina Alhaji Isah Ali Kankia da ya bayyana naɗin sabbin hakiman, waɗanda za ayi bikin naɗin a ranar 29 ga Agusta, 2026. Hakiman da za'a naɗa sun haɗa da Alhaji Sani Tukur Mu’azu Sarkin Rumah Katsina -( Hakimin BatsariDa Alhaji Abba Lawal Sani Dutsi (Gabasawan Katsina)Hakimin Dutsi, Sai Alhaji Gambo Abdullahi Dabai (Dausayin Katsina) – Hakimin Dabai akwai kuma Alhaji Zakari Maina (Dan Yusufan Katsina)Hakimin Bindawa. Da…
Read More

Tinubu ya gana da shugaban EFCC da ministan gine-gine kan kadarorin da aka ƙwace

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Talata Shugaba Bola Tinubu ya karɓi ba'asi daga Shugaban Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta'annati EFCC, Ola Olukoyede da Ministan Gine-gine da Raya Birane, Muttaqa Rabe Darma a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Rahotanni sun bayyana cewa, ganawar ta mayar da hankali ne kan gudanarwa da soke amfanin gidaje da EFCC ta ƙwace a faɗin Nijeriya, kuma ita ce ta farko tsakanin Tinubu da Olukoyede tun bayan da shugaban ya soke hukuncin hukumar na sanya wa asusun gwamnatin Jihar Osun takunkumi. Ofishin yaɗa labaran fadar ne ya fitar da…
Read More
Gidaje da dama sun rushe a Katsina sakamakon ruwan sama

Gidaje da dama sun rushe a Katsina sakamakon ruwan sama

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Katsina (SEMA) ta kai ziyarar gani da ido zuwa ƙaramar hukumar Kankia domin tantance ɓarnar da ambaliyar ruwa ta haddasa. Ziyarar ta gudana ne bisa umarnin Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa, domin duba irin asarar da aka samu tare da jajanta wa al’ummomin da iftila’in ya shafa. Shugabar SEMA, Hajiya Binta Hussaini Dan-Gani, ta ce manufar ziyarar ita ce jajanta wa waɗanda abin ya shafa da kuma tattara sahihan bayanai kan ɓarnar da aka samu, domin gwamnati ta ɗauki matakan da suka dace. Ta bayyana cewa…
Read More

‘Tsaro ba wajen taro ba ne’, Ministan Tsaro ya gargaɗi tura dakarun tsaro ana gab da zaɓe

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya) ya yi gargaɗi ga hukumomin tsaro kan dogaro da aikin tura jami'an tsaro bayar da kariya wuraren zaɓuka yayin da ake gab da farawa, yana mai cewa samun hakan ya inganta na buƙatar a ɗauki tsawon watanni ana kimtsawa. Janar Musa ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin gabatar da jawabin babban baƙo a taron Karramawa na jaridar Blueprint kan tsaro. Ya ce, wajibi ne a mu'amalanci al'amarin tsaron zaɓe wajen ɗaukar tsawon lokaci ana nazari a kai musamman don kimtsawar wuri da ƙoƙarin neman hanyoyin…
Read More

Daga ƙarshe, ɗan takarar APC Oyebamiji ya magantu bayan kaye a zaɓen Osun

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ɗan takarar gwamnan jihar Osun a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar APC, Bola Oyebamiji, ya magantu a karon fari bayan shan kaye a hannun gwamna mai ci, Ademola Adeleke a zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar. Oyebamiji ya karɓi sakamakon da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta fitar yayin da ya koka kan zargin hare-haren da aka kai wa wasu mambobin APC da magoya baya bayan zaɓen. An sanar da Adeleke na jam'iyyar Accord Party a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan samun ƙuri'a 511,067, yayin da Oyebamiji ya samu ƙuri’a 444,815 a matsayi na…
Read More

Wike ya umarci a rushe gidaje masu tare magudanan ruwa a Abuja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ministan Abuja Nyesom Wike, ya umarci a gaggauta rusa gidaje da wasu gine-gine da suke haifar da tsaiko ga a hanyoyin da ruwa ke wucewa a unguwar Maitama da wasu wurare masu fuskantar barazanar ambaliya a Babban Birnin. Wike ya bayar da wannan umarni ne bayan aukuwar wata ambaliya a kwanan nan da ta haifar da tsaiko ga harkokin yau da kullum na al'umma a sassan birnin. Ministan ya bayar da umarnin ne a yau Talata bayan ziyarar sanya ido a yankunan da ambaliyar ta shafa a Maitama, inda wani mamakon ruwan sama ya…
Read More