Labarai

Rundunar ‘yan sanda ta bada umarnin bincike kan bidiyon zargin jami’anta suna karɓar na goro a Kaduna

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda a Jihar Kaduna, ta umarci a fara gudanar da cikakken bincike kan wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, wanda yake zargin jami'an 'yan sanda suna tilasta wa masu motoci da babura ba su na goro yayin aiki a shingen bincike. Kwamishinan rundunar, Rabi'u Muhammad ne ya bayar da umarnin inda ya buƙaci a gano su waye ne daga cikin 'yan sandan aka gani a bidiyon kuma a gayyato su yayin binciken. A wata sanarwa da Kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan ya fitar a ranar Talata, rundunar ta ce…
Read More

2027: Tsohon Sufeto Janar ne zai lashe zaɓen gwamnan Nasarawa, inji Ali Bagio

Daga JOHN D. WADA a Lafiya Jibrin Ali, wanda akafi sani da Bagio babban mai goyon baya kuma mai tara kuri’u ne na musamman ga qan takarar kujerar gwamnan jihar Nasarawa a karkashin jam’iyyar Social Democratic Party SDP wato tsohon sufeton ‘yan sandan Najeriya alhaji Abubakar Muhammed Adamu inda ya bayyana cewa qan takarar nasa kadai ne zai iya lashe zaben gwamnan dake tafe a jihar. Bagio ya bayyana haka ne a Lafiya babban birnin jihar yayin tattaunawa na musamman da manema labarai kwanan nan. Ya musanta zargin cewa babban qan takarar SDP din wanda aka zaba kafin zuwan Abubakar…
Read More

Filato: ‘Yan sanda sun cafke wanda ake zargi da kitsa harin ƙauyen Mangu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'yan sanda a Jihar Filato, ta ce ta kama wanda ke zargi da kitsa mummunan harin ranar Talata da aka ƙaddamar a ƙauyen Bimper da ke Gundumar Kombun ta Ƙaramar Hukumar Mangu. Rahotanni sun ce, harin ya yi ajalin kimanin mutane 25 yayin da jikkata wasu huɗu sakamakon raunuka a farmakin safiyar. Wannan shi ne karo na uku da aka ƙaddamar da harin 'yan ta'adda acikin mako guda a Mangu. Kakakin 'yan sandan jihar, SP Alfred Alabo ne ya tabbatar da kamen ga gidan talabijin na Channels, inda ya ce a yanzu haka…
Read More

Gwamnatin Tinubu ta faɗi yadda aka sarrafa kuɗaɗe bayan tara tiriliyan N15.8 daga tallafin fetur da sauye-sauyen canjin kuɗi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnatin Tarayya ta ce cire tallafin fetur da samar da tsari guda na kasuwar canjin kuɗaɗen ƙasashen waje sun tara mata jimillar Naira tiriliyan 15.8 da ƙarin albarkatu ga ƙasa daga watan Yunin 2023 zuwa Disambar 2025, inda jihohi da ƙananan hukumomi suka samu kaso mafi tsoka. Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin Tarayya ta ce kuɗaɗen da aka samu daga cire tallafi bai shiga sahun asusun tarayya ba a ware, wato "subsidy savings", saidai an bayyana tasirinsa ta kuɗaɗen shiga da aka karɓa sakamakon sauye-sauye a canjin kuɗi da waɗanda aka samu sanadiyyar tasirin…
Read More

Sabon harin Sakkwato ya yi ajalin mutane bakwai da sace 17 a ƙauyuka uku

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu 'yan bindiga sun kai wa ƙauyuka guda uku farmaki a Ƙaramar Hukumar Wurno da ke Jihar Sakkwato, inda suka halaka mutum bakwai da kuma sace wasu guda 17 da suka haɗa da mata 15. Ƙauyukan da aka afka wa sune Dinawa, Munƙi da Gidan Dare, inda maharan suka ɗauki tsawon sa'o'i suna atisaye a daren Litinin, bayan amfani da damar mamakon ruwan sama da aka zabga a yankin. Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, Shugaban 'yan bijilante na yankin Dinawa, Aliyu Falke, ya ce an yi jigilar maharan ne a wata tirela da…
Read More

Abuja: Diloli sun shiga tsaka mai wuya bayan Wike ya haramta amfani da guraren shaƙatawa a matsayin wuraren siyasar da motoci

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Akwai yiwuwar dilolin harkar motoci a Abuja su fuskanci ƙalubale yayin da Ministan Abuja, Nyesom Wike ya umarci a gaggauta dakatar da amfani da filayen shaƙatawa a faɗin babban birnin a matsayin wuraren dillanci ko siyasar da motoci. Rahotanni sun bayyana cewa, umarnin na Wike wani ɓangare ne na ƙoƙarin Hukumar Gudanarwar Birnin (FCTA), na warware matsalolin barazanar ambaliya da ke fuskanta a sassan birnin a wannan daminar. A wata sanarwa da Jami'in Hulɗa da Jama’ar ministan, Lere Olayinka ya fitar wa manema labarai, Wike ya koka kan yadda aka mayar da filayen da…
Read More

Gwamnatin Tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi sun raba kuɗi mafi yawa a ƙarƙashin Tinubu na watan Yuli

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kimanin Naira tiriliyan 3 ne Gwamnatin Tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi suka raba a tsakaninsu daga kuɗaɗen asusun tarayya a watan Yuli, 2026, wanda ya zama mafi girma da aka taɓa rabawa a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu. An sanar da haka ne a taron Agusta, 2026 na Kwamitin Asusun Kasafta Kuɗaɗen Tarayya (FAAC) da aka gudanar a Owerri, Babban Birnin Jihar Imo, wanda kuma Ministan Kuɗi da kula da Harkokin Tattali, Taiwo Oyedele ya jagoranta. Kasafin na watan Yuli ya samu gagarumin ƙari daga tiriliyan N2.551 da aka raba a tsakanin ɓangarorin gwamnatin uku a…
Read More

Gwamnan Zamfara ya lashe kyautar gwarzon gwamna na Blueprint yayin da manyan jami’an gwamnati suka tafka muhawara kan tsaro da zaɓen 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamna Dauda na Jihar Zamfara ya samu kyautar lambar yabo ta Jaridar Blueprint ta 2026 kuma ta Gwarzon Gwamna mafi Ƙwarewa wajen Gudanar da Kuɗaɗen Al'umma da Tsare Gaskiya da Adalci, inda yake ƙoƙarin ganin gwamnatinsa ta ceto tare da sake gina Zamfara domin amfanin al'umma. Dauda Lawal ya karɓi wannan kyauta ne a ranar Talata, 18 ga Agusta yayin taron Karramawa na Kamfanin Jaridun Blueprint na Shekara-Shekara, wanda aka gudanar a ɗakin taro na Bola Ahmed Tinubu International Conference Centre da ke Abuja, inda jagororin siyasa, 'yan difulomasiyya, ƙungiyoyin al'umma, masana da sauran…
Read More

Tinubu zai yi jawabi a taron Majalisar Ɗinkin Duniya ranar 23 ga Satumba

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Tinubu zai haɗu da jagororin ƙasashen duniya a taron Majalisar Ɗinkin Duniya (MƊD) karo na 81 (UNGA 81), inda aka tsara zai gabatar da jawabi a New York, a ranar Laraba, 23 ga Satumba, 2026. Manhaja ta ruwaito cewa, an zaɓi Tinubu ne matsayin mai jawabi na 10 yayin zangon safe a rana ta biyu ta babban taron tafka muhawara (high-level General Debate), wanda za a gudanar a tsakanin ranakun 22 da 28 ga Satumba a hedikwatar Amurkan. A yadda aka tsara, Shugaban Nijeriyar zai yi jawabin nasa ne yayin zangon safe,…
Read More

‘Yan bindiga sun halaka sufeton ‘yan sanda da wasu huɗu a sabon harin Adamawa

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu 'yan bindiga sun halaka sufeton hukumar 'yan sanda da wasu mutane huɗu a yayin wani hari da suka ƙaddamar a ƙauyen Gaya Dlang da ke Gundumar Kuva Gaya a Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa. Al'amarin ya auku ne da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Litinin, wanda kuma shi ne mummunan hari na biyu da aka samu cikin wata guda, kuma a haifar da fargaba acikin al'umma bisa hare-haren 'yan bindiga. Kakakin Runndunar 'yan sandan jihar, SP Suleiman Yahya-Nguroje ne ya sanar da haka yayin ganawa da wakilin gidan talabijin na Channels…
Read More